******SALON SO******* 1 to 6 :********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** : BY SULAIMAN BOMBOY. . Kyakkyawar yarinya ce 'yar kimanin shekara goma sha bakwai, direbanta ya yi parking da mota ya zagayo ya bude mata ta fito ta shiga cikin wani hadadden gida kerarre, ke da kallon tsarin ginin kin san hoto ne daga kasar waje aka yi irin sa. A kofar falon ta yi sallama ta shiga. Matar da take hakimce akan kujera cikin tsantsararriyar kwalliya ta kece raini, tana ta girgiza kafa da wayar sadarwa a hannunta da take hira. Tana ganin shigowar yarinyar ta dire wayar cikin fara'a ta tare ta, tare da cewa, "A'a Jawahir 'yar Dady yau a gari? Ko dai batan kai kika yi ne?" Jawahir ta yi murmushi yayin da ta durkusa gabanta ta ce, "Aunty ina yini?" "Lafiya lau Jawahir, amma dai a nan za ki kwanar min ko.? Tun da gobe ba ku da makaranta." Jawahir ta yi dariya tare da cewa, Tafiya zan yi Aunty yau Dady zai dawo daga saudiya, da kuma ya dira a kasar nan ni zai fara tambaya, kuma ni ma ba zan so ya dawo ba mu hadu ba. Aunty ta yi murmushi ta ce Jawahir gidan Daddy ke dai kullum kina like a gida kamar daddawar daka ba kya son zuwa ko ina ko?" Amma zan je na samu mommy dinki na ji ko ita take hana ki zuwa." Jawahir ta yi murmushi, "Wallahi Aunty babu rawan mommy Daddy na ne baya son na rinka fita. Sallamar da ta ji ce ta sa ta yin shiru, sai da aka amsa masa sannan ya shigo. Ya zauna a kan kafet tare da rissinawa ya gaisar da Aunty. Aunty ta amsa cikin kulawa ta musamman ta kalle shi ta ce, Ba dai har ka dawo daga office din ba?" "Wallahi Aunty vacci nake ji shi ya sa na taho gida don na kwanta na huta." Aunty ta girgiza kai tare da cewar, "Ba ka kula da bakuwa ba ne?" Sai sannan ya kalle ta ya ce, "Wallahi ai kamar jawahir ko.?" Au ka mance ma? To ita ce, Jawahir ta dan rissina ta ce, "Yaya Haidar ina wuni?" Ya amsa cikin kulawa sannan ya ce, "Ya su Dady?" "Daddy ba ya kasar, yau dai muke sa ran dawowarsa." "To Allah ya dawo da shi lafiya, Abin da Haidar ya ce kenan ya mike ya nufi sashensa. Jawahir ta mike Aunty zan tafi" "Haba jawahir har tafiya zaki yi.?" "Wallahi Aunty tafiya zan yi doki nake yi ne na je na fara shirin tafiya taryar Daddy. "To 'yar Daddy ki gaishe min da shi, kafin na zo gobe yi masa sannu da zuwa. "Ta fito da sauri, direbanta ya karbi kayan da yake hannunta ya zuba a but ya bude motar ya shiga ya tayar suka miki hanyar gida +++++++++++++++++++++ Alhaji Ibrahim shine mahaifin Jawahir, mutumin kirki ne, akwai shi da son jama'a ga yawan kyautatawa na kasa da shi, sam ba shi da kyamar talaka. Yana da dadin zama idan ka kiyaye abubuwan da ba ya so, na farko ba ya son raini, kuma shi kaifi daya ne, in dai ya ce, "I, ko "A'a" to ba wanda ya isa ya tankwara shi sai uwarsa. Su uku ne a wajen iyayensu, shi ne babba sai Aisha wato Aunty babar Haidar sai Aminu, wanda shi ne autansu. Ubansu da suke kira da Baffa ya dade da rasuwa sai mahaifiyarsu Rahmatu da suke kiranta da Inna. Inna mace ce mai kirki da hakuri ga ta da son zumunci, duk inda aka ce ga dan uwa ko ta yaya suka hadu ta jawo shi a jiki ita bare ma jawo shi take yi don ya zo ya ci arzikinta. Tana zaune a unguwar sabon tatin mandawari. Tana matukar son jawahir don a cikin jikokinta babu wanda ya kama kafar son da Inna take yi wa jawahir. Alhaji ibrahim matarsa daya Hajiya Hafsatu, ita ce mahaifiyarsu Jawahir, suna ce mata Mommy. Mommy tana da 'ya'ya shida biyar maza daya mace. Akwai Abba me sunan kakansu sai Abdullahi, sai Nasir, sai Jawahir da Auwal da Sani. Jawahir ita ka dai ce mace a gidan, kowa ji yake da ita ba ma kamar Alhaji ibrahim da yayyanta. Suna son ta suna shagwabata amma duk da haka ba ta sangarce ba don tana tsoronsu tana kuma jin maganarsu. Jawahir yarinya ce kyakkyawa tana da hankali da nutsuwa akwai ta da biyayya ba ta da rowa. Sai dai miskila ce ba kowa take iya sakewa da shi ba, ba ta fiya son magana sosao ba, in kinji hirarta ce ne da Daddynta ne ko yayyanta sai mommynta, to shi ne za ki ji har da dariya. Amma shagwababbiya ce ta kin karawa don ita har kannanta Auwal da Sani shagwaba take yi musu bare kuma su Yaya Abba da uwa uba Daddynta. Bayan Auwal ne ya dauke min babban turarena da ya fi kowanne tsada. Shi ne kike kuka? Rabu da shi zai gamu da ni ne je ki cikin dakina kan mudubi ki zabi wanda kike so share hawayenki ki yi dariya. Ta fada dakin Dady da gudu tana murmushi yaya Abba ya ce, Su jawahir sarkin rigima. Shi kuwa Haidar a zuciyarsa cewa ya yi, Kai wannan yarinyar tafi ya shagaba shi ya sa take ba ni haushi sai na ga kamar na doke ta in ana lallabata. Yarinya sai shagwabar tsiya sai ka ce ita ce Auta." Tunaninsa ya katse ne a dai dai lokacin da jawahir ta fito daga dakin, hannunta rike da sunkumemen turare. Ta nunawa Dady ta ce, Dady ga shi na dauka. Yace, "To 'yar Dady ya yi miki wannan din?" Ta daga kai, "To maza ki je ki boye abunki ki ta fesawa. Ta durkusa fuskarta cike da murmushi ta ce,Na gode Dad Allah ya kara girma, Ya shafa kanta yana murmushi ta yi waje a guje. Takaici ya cika Haidar a zuciyarsa ya ce, Ya za a yi ma wannan 'yar yarinyar a ba ta wannan turaren? Ya za ta yi da shi? don kudinsa wajen dubu goma sha biyar ne,to ita ta san darajar kamshin ne ma. Yanzu haka wasanta za ta yi da shi kawai. Yaya Abba ya girgiza shi tare da fadin, Haidar me kake tunani ne? ko ka tuno America ne? da yake tare suka yi karatu a can shi da Haidar din. Dariya suka yi suka tafa. Kiran sallar da aka yi ne ya sa su tashi don zuwa su ba da farali. To irin wannan halayyar ta Haidar ita ce take bawa jawahir haushi don haka ko gidansu ya zo ba ta kula shi karkari ta ce masa ina wuni ta wuce shi ba tare da ta jira amsarsa ba. Dan mulki kenan. Ita jawahir duk da miskilancinta ba ta da daukan kai kuma akwai ta da yi wa mutum murmushi tana da halin kyauta duk inda ta ga talaka ko kaskantacce in dai ta san mai bukata ne, to za ta gayawa Daddy ya taimaka musu. wannan halayya tata ita take kara sa kaunarta a zuciyar Daddynta. Kamar yau da safe jawahir ta gama baccinta ta fada toilet a yi wanka ta fito ta tsaya gaban mudubi aka shiga kalailayar jiki, a shafe nan a goge can, ta tsara kwalliyarta cikin boyal shudi rigar fitet da zane ta sa hadadden fashion dinta yari da sarka da abin hannu me shudin dutse, Daddynta ne ya siyo mata daga london. Ta hadu iyakar haduwa fuskar tata sai sheki take yi ta feshe jikinta da turaruka ta fito ta nufi sashen Dady. Ta kwankwasa ya yi mata izini ta bude ta shiga. "A'a 'yar Dady kwalliyar ta yi miki kyau, Ta yi murmushi ta durkusa ta gaishe shi, "Don Allah Dady ina so yau zan je gidan Inna. "Kin sani jawahir ba na so ki rinka yawan fita amma tun da gidan Innata za ki je ba komai sai ki je. To me za kaiwa Innan? Jawahir ta dube shi tana murmushi ta ce, Dady duk abin da ka ba ni. To shi ke nan 'yar gidan Dady, daman ke ake jira tashi mu je a yi brek. Mominta ta fito daga cikin dakin Dadyn cikin rantsatsiyar kwalliya kamar me shirin zuwa fati. Jawahir ta yi saurin zubewa ta gaishe ta, mommy Daddy ya bar ni zan je gidan Inna Ta ce, "Yauwa koke fa, ai gwanda ki je kusan kullum Inna sai ta yo miki waya ta ce ba ta jin dadi idan ta dau lokaci ba ta ganki ba. Suka fito babban falo suka hau tabir inda 'yan samarin suke jiransu. Jawahir ta gaida Yayyanta inda ita kuma kannenta suka gaishe ta, al'adar gidan ke nan kowa sai ya gaisar da wanda ya girme shi. Ta kalli Nasir ta ce, "Yaya Nasir za ka kai ni gidan Inna? Ya harare ta, Ni direbanki ne ina amfanin Idi direban da aka ajiye muku?" Yaya Abba ya ce, Wai kai me ya sa kake haka ne? duk yanda direba zai kula da ita ai ba kamar dan uwanta ba ko? Ki bari mu gama break sai na kai ki. Ta ce, "Yauwa Babban Yaya na gode Iyayen dai suna jinsu ba su tanka musu ba. Bayan gama break dinsu jawahir tanufi dakinta ta kara gyara fuskarta ta sako shudin takalmi da shudin mayafi ta fito, Dady za mu tafi," To me za ki kaiwa Innarki? shiga sito ki jido mata abin da kika ga za ki kai mata Nasir ya ce, Wallahi Dady sito din Inna cike yake da kayan abinci da na masarufi. ka manta shekaranjiya ka ba ni kayan abinci da na amfani mota guda na kai mata? kuma da muke zuba mata a sito din ma akwai wasu a ciki. Abba ya ce, To sai a kai kudi kawai. Momy ta ce, Ki je wajen Rahane me aiki ini ta gama gasa kaji dana sa ta da akwai cake da samosa da na bayar akayi mata, sai soyayyiyar miyar zabi dana yi mata tun jiya. Alhaji ya ce, Wallahi dalilin da ya sa kenan kullum Hafsa nake kara son ki, kike dada shiga rai na don duk hanyar da za ki faranta min kin san ta, ga yanda kike kula da mahaifiyata, ni kuwa me za ki nema a wajena na kasa yi miki. Ta yi murmushi, Ba komai Alhaji Inna ai uwatace, ba abin da ba zan iya yi mata ba, don albarkarsu muke nema. Auwal da sani su ma suka ce, Dady mu ma za mu je gidan Inna. Jawahir ta turo baki, Gaskiya Dady ba za su bi ni ba, damuna za su yi ta yi da hayaniya sun fiya surutu. Dady ya ce, Ku yi hakuri Auwal ma je da ku da daddare, kun ga islamiyya za ku je in karfe biyu ta yi ku kyale ta ta tafi. Yaya Abba da jawahir suka fita suka nufi gidan Inna Yana tsayawa da motar ta fito a guje za ta shiga cikin gidan Abba ya kira ta, Zo ki debi wasu kayan mana. Ta ce, To suka kwashi kayan suka yi ciki. Salamu alaikum 'yar tsohuwa, kina nan?" "A'a wa nake jin magana kamar bera?" Kai Inna ki ga zankadediyar budurwa ki ce mata bera.?" Inji yaya Abba. Inna ta ce, Ai lallai kuwa 'Yar dady ta girma don ko yanzu ma a ka yi mata aure ai zama za ta yi. Jawahir ta rufe fuskarta da hannuwanta ta ce, Haba Inna yarinya ta da ni ni da ko saurayin ma ba ni da shi." Inna ta ce, "A'a ba kya dai kula su ga Hafizu abokin Abba nan duk nacin da yake yi kin ki kula shi." Jawahir ta ce, Ai ke kuma yanzu kin ga za mu bata. Abba ya duba agogo ya ce, Inna ni zan wuce office. To maigidana sai ka dawo. Yaya Abba ya tafi. Jawahir tana cinyar Inna tana yagar cinyar gasasshiyar kaza suna ta zuba hira. A hankali aka yi sallama a kofar falon aka shigo cikin takama da isa. Jawahir sanin me shigowar ne ya hana ta amsa sallamar bare ta dago kai ta kalle shi. Inna ta kama washe baki, "A'a yau saraki ne a gidan tsohuwa? Lallai kam batan kai aka yi. Yayi kasaitaccen murmushi ya durkusa gaban Inna ya gaisheta, ta ce, Bature ba a ganinka sai an cike form ko? Yayi kasaitaccen murmushi ya ce, Inna sai dai idan ba a so ganin namu ba. Ta ce, Wai yaushe za ka yi aure ne? ko so kake yi ka za ma tuzuru? Ya ce, Inna me kike ci na baka na zuba, kwanan nan zan kawo miki dakakkiyar yarinya 'yar jami'a me cikakken ilimin boko wayayyiya. Inna ta ce, Ba dai cikakkiya ba sai ka kwaso min kwaila. Ya ce, Haba Inna me za ayi da kwailar mace, duk yarinyar da ba ta je jami'a ba ai ba ta waye ba namijin ya sha wuyar zama da ita, don hauka za ta yi ta yi masa." Jawahir ta san duk da ita yake wannan habaicin maganar ita kuwa ko kallo be ishe ta ba. Inna ta ce, Jawahir kina kallon Yayanki ba za ki gaishe shi ba.? Jawahir ta yamutsa fuska tare da kau da kai gefe daya ta ce, Ai ban gane shi ba ne, Maganar ta yi masa ciwo amma da yake ba da shi ake maganar ba sai ya yi shiru yana jin su. Inna ta ce, Kin ci gidanku, in.. ban da iya shege yaya za ayi ke da dan uwanki ki ce baki gane shi ba?" Jawahir ta ce, To in ban da abinki Inna ai sai kana yawan ganin mutum za ka san shi ko.? Inna ta ce, Ba na son dogon surutu, ni dai ina horonku da ku rike zumunci, don zumunci ba abin wasa ba ne, don Allah Subhanahu wata'ala ya ce, Duk wanda ya yanke zumunci ba shi ba rahamar Ubabgiji. Jawahir ta ce, Inna ni fa ba yanke zumunci zan yi ba, gane shi ne kawai ban yi ba, to ba sai a yi min bayani ba. Ya mike, "Inna bari na karasa office." To Haidar ba a abin da za kaci a gidan tsohuwa,. Ya girgiza kai tare da yamutsa fuska, Inna ba zan iya cin komai ba a nan don zuciyata tashi take yi. Ya bawa inna kudi ta yi masa godiya tare da sa masa albarka. Ya yi gaba jawahir ta mike ta ce wa Inna bari na raka shi bakin motarsa. Inna tace, Yauwa ko ke fa, ai gwanda ku rinka karfafa zumunci, don bi so nake kullum na ga kanku a hade. Jawahir ta same shi a harabar gidan yana kokarin bude motarsa ya shiga, Jawahir ta ce, A dai taka a hankali a daina jin kai da wulakanci, don duniyar ba matabbaciya ba ce, wata rana a karkashin kasa za a saka mutum. Ya kalle ta ya yatsuna fuska tare da zuba mata harara ya tofar da yawu gefe daya ya sa hannu ya toshe hanci wai doyi take yi. Ta yi shigewarta ciki ta bar shi a wajen yana kokarin shiga motarsa. A zuciyarsa ya ce, Lallai yarinyar nan ba ta da kunya amma zan yi maganinta ne,. Jawahir sun zana jarabawar fita daga Secondary har sun hada fatin gama secondry. Duk yawancin samarin da suke kawo kansu gare ta ba ta kula kowa sai wani Faruk da jininsu ha hadu daga mutunci suka zarce da soyayya. To suna son junansu don duk yanda jawahir take kin samari da an ce Faruk zai zo kaga rawar kai da girin girinkidishin yin tsararriyar kwalliya ta taron masoyi. Sannu sannu soyayya mai zurfi ta shiga zuciyarsu. ****************************** Aunty tana zaune a falo Abvan Haidar ya fito daga toilet ya zauna kusa da ita ya ce, Kin sani ne, Wallahi tun satin da muka je saukarsu Jawahir zuciyata ta matsu da sha'awar halayyar yarinyar nan. Tana da hankali da nutsuwa ga girmama nagaba da ita. Abin da ya fi bani sha'awa da ita yanda take karatun Alkur'ani a wajen saukar nan tasu, ta iya fitar da harafi ga zakin murya da bawa kowanne baki hakkinsa. Ni yanzu shawarar dana yanke zan je na samu Alhaji ibrahim da ya tallafa ya bawa Haidar auren jawahir. Aunty ta yi ajiyar xuciya ta ce, Wallahi da hakan za ta faru da na fi kowa farin ciki, amma abin da nake tunani Alhaji anya kuwa hakan za ta yiwu ka san halin miskilancin danka kada ya ki a zo zumincinmu yana baci a banza, gaskiya Alhaji ka duba ka gani." Ya ce, Karki damu Aisha, Allah ya ga niyarmu ta kara donkon zumunci ce a tsakaninmu, insha Allahu ba za su bamu kunya ba. Ta ce, To shi kenan Allah ya taimaka, Ubangiji ya sa a yi a sa'a amin Da magariba Abban Haidar ya nufi gidan amininsa Alhaji ibrahim. Suka karbi junansu da murna da farin ciki. Suna sitting room dinsa. suna yin sallar insha'i a masallacin gidan suka dawo sitting room din suka ci abinci. Daga nan Abban Haidar ya zayyanawa Alhaji ibrahim shawarar da ya yanke na game da hada 'ya'yansu aure jawahir da Haidar. Alhaji ibrahim ya yi dariya ya ce, Amma na ji dadi. Gaskiya wannan ai shawarace me kyau. Allah ya tabbatar mana da alherinsa, to amin. Allah ya sa ayi da mu." Ko da Abvan Haidar ya tafi Dady ya shiga gida ya gayawa mommynsu jawahir komai. ita ma addu'ar ta yi tare da sawa abin albarka. Da safe bayan sun kammala break dinsu. Alhaji ibrahim ya kalli jawahir ya ce, To jawahir a yau nake son sheda miki lokacin aurenki fa ya yi, zan aurar dake don cika unarnin Allah subhanahu wata ala. Ta dafe kirji. Dady shekarata goma sha bakwai fa." Ya ce, To menene, ai kin isa ko ba ki da saurayi ne?" Ta boye fuskarta a cikin hannuwanta ta ce, Daddy akwai Faruk, amma ce masa nayi ya dakata sai na fara zuwa jami'a tukunna na yi masa magana ya fito. Alhaji ta ce, Uhm jawahir ki kyale maganar Faruk ki ba shi hakuri kawai don ni na riga na yi miki miji. Ta dafe kirji cikin kwalalo ido ta ce, Na shiga uku sai kuma kuka don Allah Dady ka yi hakuri ka bar ni na auri Faruk shi zuciyata take so." Alhaji ya girgiza kai, Kada muyi haka da ke, ki yi hakuri ki bi umarnina ki auri mijin dana zaba miki, insha Allahu ba za ki taba da na sani a rayuwarki ba, kin ji. Ta dafa kanta. Ta amsa da To Dady Allah ya zaba mana mafi alheri, Ta mike ta yi dakin mommy tana kuka. Momy ta ce, Lafiya ke kuma kike kuka? Ke da wa? Me aka yi miki? Mommy ki taimake ni Dady zai yi min auren dole, Ta kwashe komai ta gaya mata. To ke tun dsya ce yayi miki miji to ki hskura da Faruk din mana. Jawahir ta kuma fashewa da kuka, Don Allah momy ki taimaka min ya bar ni na auri Faruk. Momy ta ce, Kin ga kawai hakura ki bi zabin mahaifinki ni ba ruwana ina zaman lafiya ba za ki jawo min tashin hankali ba. Ki bari zan yi nafila da addu'0'i zan miki istihara don neman zabin Ubangiji, amma ba na so ki tayar da hsnkali, don komai mukaddari ne daga Allah, kin ji,ki share hawayenki kar ya gane har yanxu kuka kike yi. Ta ce,,To momy ta mike ta nufi dakinta. ****************************** A gidan Haidar kuwa Alhaji ya gama gayawa Aunty yanda suka yi da yayanta. Aunty ta ce Nina san yaya zai amince ni dai tsorona yaron nan ka san jin kansa kar a yi auren ya zo yana wulakanta min 'ya." Alhaji ya ce, Kirawo min shi mu ji ta bakinsa, ta daga waya ta danna lambobinsa ta yi ringin ya fi sau nawa kafin a daga sai can ya daga. Hello wallahi ban san ke ba ce sai da na kalli wayar sai na ga lambarki lafiya Aunty.?" Lafiya kalau ka zo falo Abbanka yana son magana da kai yanxu" To Aunty ga ni nan zuwa Suka ajiye kan wayar. ya yi sallama tare da tura kofar ya shiga bayan sun amsa masa, Ya zauna gaban Abbanshi a kan kafet, Abba ga ni. Ya ce, Yauwa Haidar na kirawo ka ne daman don na ji ko ka tsayar da matar da zaka aura? Haidar ya ce, Wallahi Abba ni ba ni da lokacin kallon matan ma bare na ga wacce ta yi min. Alhaji ya ce, Ni kuwa ka ga ina da lokacin kallon su, don har na samo maka matar da za ka aura, don nasan za ta yi maka yar uwarka ce Jawahir." A firgice ya daga kai ya kalli Aunty ya ga karatunta ma take yi ya juya ya kalli Abbansa ya ce, Abba jawahir fa ka ce, Haba Abba me zan yi da wannan kwailar yarinyar, yarinyar karama zan aura? Haba 'yar da ko kilewa ba ta yi ba, kwanan nan fa ta gama secondary. Alhaji ya daga masa tsawa, Kai ba ma son zancen banza, ni ita na zaba maka kuma ita nake so ka aura ta zamo uwar 'ya 'yanka. Haidar ya marairaice kamar zai yi kuka, Wallahi Abba jinina bai hadu da yarinyar ba ta da kunya shi ya sa na tsane ta. Aunty ta zaburo ta rufe shi da fada, Yar tawa kake cewa marar kunya ka tsane ta? To bari ka ji na gaya maka ko kana so ko baka so aure bsbu fashi, munyi niyyar hada ku kuma sai mun yi, in ya so ranar da aka kai ta dakinka ka yanka ta gunduwa gunduwa ka kawo mana namanta, wannan shi ne maganin kiyayya marar kunya wanda bai san mutunci ba. Abba ya dakatar da ita, To fadan ya isa haka, na san bai yi dai dai ba amma ki yi hakuri. Ya kalli Haidar, Ka tashi ka tafi amma ka sani jawahir ita ce zabinmu ba gudu ba ja da baya, sai ka je ka yi tuananin abin daka ya fi dacewa da rayuwarka. Haidar ya taso cikin bakin ciki, zuciyarsa tana kuna ya yo dakinsa yana magana a zuciyarsa yana zagaye falon nasa maganar har ta fito fili. Haka kawai a rasa yarinyar da za a ce na aura sai wannan figaggiyar yarinyar 'yar karama, yarinyar da muka yi rainonta? me zan ji a jikin wannan kwailar, yarinyar da kyar ma in ta fara kirgar dangi? Haba ai an cuce ni, yanda nake ji da kaina nake so na auri katuwar mace wadda ta gama jami'a me hankali wadda za ta fuskanci halina ta bi ni yanda nake so mu zauna lafiya yaushe za a hada ni da wannan faratun? Yarinyar da ba ta fi ta tsaya min iya ciki ba, gaskiya a canja shawara, don in har yarinyar ta yarda ta aure ni sai ta gane kurenta. , To ya mu ci gaba ko 11 décembre 2016, 19:48 · Public *******SALON SO***** ****PART 7 TO 10**** : BY SULAIMAN BOMBOY. . Da Alhaji ibrahim ya gayawa inna shawarar da suka yanke na hada Haidar da jawahir aure, Inna ta yi murna ta yi godiya ga Allah ta sa wa abin albarka burinta zai cika ke nan na hade kan zuri'arta. Bayan Alhaji ya dawo yana cikin iyalinsa suna hira ya kalli jawahir ya ce mata, Jawahir dan uwanki fa na zaba miki wanda za ki aura, wato Haidar Cikin fargaba da tashin hankali ta wuntsilo daga kan kujerar da take zaune ta dirkushe a gaban Uban tana kuka ta rike kafafuwansa tana rokonshi, Don Allah Dady ka yi min rai kayi hakuri kada ka aura min yaya Haidar, wallahi ba ya so na ba ya kaunata, ba ma shiri da shi. Dady kada ya je ya shake ni namutu Dady ku yi asarata. Ba abin da zai faru jawahir yana son ki ba zai yi miki komai ba, ki yi biyayya a gare mu insha Allahu za ki ga kyan abin kin ji.?" Ta daga kai ta mike ta yi dakinta tana kuka mai ban tausayi ga mai sauraro. Momy ta kalle shi ta ce, Dan Allah ka hakura da auren nan tun da yarinyar ba ta so kuma yanzu an daina yayin auren dole." Ya yi saurin daga mata hannu, Dakata don Allah ba na so ki ari halin da ba naki ba ki sawa kanki. komai da kika sani mukaddari ne daga Allah, yanda nake son jawahir ba zan taba cutar da ita ba, ko na kai ta inda za ta cutu ba. Ki sani duk wani Uba an fi so ya zabarwa 'yarsa miji na gari, ki yi la'akari da shekarun jawahir sha bakwai fa, to a ina ta ga hankalin da tunanin da za ta iya zabawa kanta miji na gari? Ki yi hakuri ki barwa Allah zabinsa Momy ta ce, Shi ke nan Alhaji Allah ya zaba mana abin da ya fi alheri Cikin lokaci kankani an kawo kudi har an sa ranar aure wata biyu kacal. Hankalin jawahir ya kara tashi duk ta fige ta rame ba ta da aikin komai da ya wuce kuka kullum. Ita ta kasa zuwa ta gayawa Dadynta a fasa auren nan do ita ba yanda za a yi Dadynta ya gaya mata magana ta tsaya ja in ja da shi, don haka yamma tana yi a surare ta yi gidan Inna A gigice ta shiga kowa ya kalle ta ya san tana cikin tashin hankali. Inna ta tare ta cikin tsoro da tashin hankali tare da cewa, Ke kuwa yarinyar nan me ya same ki haka kika yi irin wannan ramar haka? Jawahir ta saki wani tsumammen kuka, hankalin Inna ya kara jagulewa tana tunanin ko wani ne ba shi da lafiya ko mutuwa aka yi musu. Ganin yanda Inna ta rude ne ya sa ta yin shiru amma idanuwanta be daina zubar da hawayen ba, Inna ta ce, Jawahir me yake faruwa ne? Ki gaya min waye ya mutu?" Jawahir ta ce, Don Allah Inna ki hana Dady ya hada aurenmu da yaya Haidar wallahi inna ba ma son junanmu ko kadan ni da shi halinmu be zo daya ba, irin rayuwar kowanne daban. ko an yi auren ba dadin zama da juna za mu ji ba. Inna da a zo a na bata zumunci ai gwanda ma kada a yi ko ba gaskiya ba? Inna ta yi shiru kamar ba za ta yi magana ba, jawahir ta suka daga kujerar ta rirrike kafar Inna tana gunjin kuka, Ki taimakamin inna kada rayuwata ta salwanta. Inna ki yi wa Dady magana ya janye maganar aurenmu. Innata kamo jawahir ta rungume ta tana rarashinta ki yi hakuri jawahir, komai nufin Allah ne, ba na son yin shisshigi a lamarin aure, don ba mu san abin da Allah ya boye ba, amma zan yi kiran Alhajin na yi masa maga.......sallamar Haidar ce ta katse mata zancenta. Ya shigo wujiga wujiga kamar wanda aka jefo har ya furgitar da Inna. Inna ta ce, Lafiya Haidar me ya same ka haka duk ka yankwane kamar marar lafiya.?" Ya ce, inna. Abba da Aunty sun takura min wai sai na auri waccan kwailar yarinyar. Inna ki dube ni yanda nake a rasa wanda za a ce na aura sai wannan tatsitsiyar, haba inna gaskiya ba a yi min adalci ba." inna ta daga masa hannu ta ce, "To ya isa haka ka je gida ka kirawo min Auntyn taka. Ka biya gidan kawun naka ka kirawo min shi, ina son ganin sa. ya ce, "To ya yi waje cikin fushi. Jawahir ta sake fashewa da kuka ta ce Inna kin ji irin wulakancin da yake yi min ko, wai ba zai iya fadar sunana ba sai dai ya ce min kwaila ko tatsitsiya amma ake kokarin lika min shi haba inna ai ba ayi min adalci ba. Inna ta ce, "Ki yi hakuri bari su zo sai a san abin yi. Bayan sllar magariba Aunty ta iso shi kuwa Dady sai da aka yi sallar insha'i amasallacin gidan inna sannan ya shigo cikin gidan tuni daman jawahir ta koma gida haidar kuwa daman bai dawo ba. Bayan gaishe-gaishe da wasa da dariya na uwa da ya ya, Inna ta yi gyaran murya ta ce, " Daman abin da ya sa na tara ku game da maganar auren yaran nan ne. Inna ga a hakura da hadin nan kada zumuncin da ake ta ikirarin ya zo yana lalacewa. Dady ya ce, " Inna duk ki rabu da yaran nan insha Allahu hadin auren nan nasu babu abin da zai jawo mana sai alheri saboda bayan ranmu zumuncinsu ba zai lalace ba. Amma yanzu ba kwa ganin yanda ba su damu da junansu ba, nan gaba abin ya zame musu gaba me karfi. Inna tace, "Gaskiya haka ne. Aunty ta ce, "To yaran nan fa mu muka haifesu ba su suka haife mu ba, to don me za mu bi son rainsu bayan mun san gaskiyar magana inda take Inna ta ce, to shi kenan Allah ya yi mana zabi na alheri suka yi addua suka shafa kowa ya nufi gidansa. Yau da gobe taki wasa kwance ta shi babu wuya a wajen Allah cikin ikon Allah lokacin biki ya zo ana ta shirye shiryen biki. Biki ne da yaye da 'yan uwa suke ta yi masa shiri na musamman wanda za mu ce su kadai suke yin abinsu, don Ango da Amarya na cikin mummunan bakin ciki da bacin zuciya. Ba yanda ba a yi d a jawahir ta je ta rabawa kawayenta katin biki ba amma taki da ta ga ma za a matsa mata sai ta gudu gidan inna. Da inna ta yi mata maganar rabon katin bikin sai ta sa mata kuka dole sai aminiyarta ce da manyan kawayenta suke ta shige da fice na bin kawayen duk inda suke suna kai musu katin biki na gayyata. ******** ******* ******** ********* ********* Bangaren Angon kuwa Haidar abun duniya duk ya dame shi, ganin da gaske suke lamarin nan ba za su fasa aura masa wannan kwailar yarinyar ba. idan ya zauna shi kadai yana yawan tambayar kansa cewa, "Wai su abba me suka gani ajikin jawahir har suke kokarin aura masa ita? wayarsa ce ta yi kara yana dubawa ya ga Abbansa ne da sauri ya amsa, "HELLO ABBANA. Abban ya ce, "Ka zo yanzu ina son ganin ka a falon sama." "To abba ga ni nan zuwa. "Ya mike cikin hanzari ya nufi bangaren babanshi ya hau samansa. "Assalamun alaikum." "Alaikas salamu, shigo Haidar. Aka amsa masa tare da ba shi umarnin ya shiga . Haidar ya shigo ya durkusa a gaban Abban nashi ya ce, "Abba gani. Abban ya ce haidar me kake so ka nuna min ne? kana so ka tozarta ni a idon duniya su san ban isa da kai ba?. Ya dago a firgice ya ce Abba me ya faru kuma? haidar na nema maka auren yarinya ka ki kula da lamarin ga shi yau saura kwana biyu daurin aure, babu wani shiri da kake yi. Yanzu da ba dan na bawa abokinka katunan daurin auren ya rabawa abokananka ba da haka za a daura maka auren ba abokin ango ko daya, kuma ko wajen jawahir din baka je ba bare ka san me take bukata da za ka ba ta ko? Haidar ya ce, ka yi hakuri Abba ganin dana yi kuna tsaye akan komai duk kun gama wani shiri da zan yi shi ya sa ban mayar da kai ba, amma don Allah Abba ka yi hakuri in an jima zan je gidansu jawahir din don na ji abin ta take bukata. "Yauwa Haidar ko kai fa Allah ya yi muku albarka . Ya dauko kudi dubu dari ya ba shi to Haidar ga wadannan sai ka ba wa jawahir din. "Abba da ka bar shi ga kudi can da na ware zan kai mata na shagalin 'yan mata kawayenta. Ba komai hada ka kai mata gaba daya ai abubuwan shagalin da yawa. "To Abba an gode, Allah ya saka da alheri. Amin dana Allah yayi maka albarka. Da yamma Haidar ya gama shirinsa ya hau motarsa ya nufi gidansu jawahir. Ya tura maigadi ya yo kiranta . maigadi ya daga waya ya buga cikin gidan mummy ce ta dauka. maigadi ya rissana ya gaisheta kamar tana kalonsa sannan ya fadi sakon Haidar na son ganin jawahir. momy ta ce Ai ba ta nan tan gidan inna maigadi ya gayawa Haidar to sai Haidar din ya shiga ya gaisa da momy ya fito ya nufi gidan Inna. Yayi sallama falon ya shiga ya ga jawahir kwance kan cinyar Inna ya kalle ta ya doka tsaki. A zuciyarsa ya ce, "Sangartacciyar yarinya in an yi auren na ga jikin uban wanda za ki hau. Inna ta ce, "Lafiya daga shigowarka kake tsaki?" yace, "Bakomai inna suka gaisa suna hira tare ya dan taba wasan jika da kaka ya ce, "Inna tursasani fa aka yi na zo wajen waccan. Inna ta ce, "Ai ga ta bari na bagu waje. yace a a inna ki yi zamanki ba sai kin tashi ba, ji zan yi dame da me take bukata. Inna ta ce bari na fita kwafi jin dadin sakewa." Sunfi tsawon rabin awa ba wanda ya ce da kowa komai, Haidar ya kalli ta ya ya mutsa fuska tare da tabe baki ya yi tsaki, "Ke in banda kinci albarkacin iyayenmu da sai kin raina kanki, don ni banga abin so a jikinki ba. Domin baki da cikakkiyar surar dazaki ja hankalina. Don haka ma in kin shigo gidan sai kiyi hakuri da irin zaman da za kiyi don ba wai wani abu ne zai shiga tsakaninmu ba. Ya debo kudin da Abban ya bashi dubu dari ya jefe tada su. "Ga shinan ba don halinki ba kuma wai a aljihuna na baki ba Abba ne ya bayar a kawo miki tatsitsiyar kawai." Yayi daya falon da inna tashiga yayi mata sallama, "Inna mun gama zan tafi don akwai ragowar shirin da ban kammala ba. Inna ta ce, "To Haidar a sauka lafiya, ya fito da kudi dubu hamsin ya ba ta ga wannan inna ke ma kya yi hidimar bikin. "To duk ni kadai Haidar ? to na gode Allah ya saka da alheri, ubangiji ya albarkaci wannan auren naku. Shi dai ya yi ficewarsa . INNA ta shigo gurin jawahir ta kula da halin datake ciki don saboda tsananin bakin ciki da takaicin da haidar ya haifar mata sai ya hadu ya dunkule mata a kirji ga hawaye ya ki fitowa bare in ya zuba ta ji sa 'ida. Kan ka ce meye wannan kirjinta ya hau zafi ga ba daya jikinta sai ya hau kakkarwa yana bari. inna ta rikice tana cewa, "Lafiya jawahir, yanxu fa na barki kalau dake me ya same ki.? Ta nunawa inna kirjinta ta ce inna kirjina ne yake ciwo, "Da kyar take iya maganar. sai numfashinta yakoma fita sama sama, ba jimawa abu ya ci tura idan ta ja numfashin sai ya dade be dawo ba. Hankalin inna ya yi masifar tashi ta kidime da kyar ta iya kiran direbanta a waya ta kira shi ya zo da sauri suka hadu suka kinkimi jawahir suka sa ta a mota inna ta shiga ya ja suka tafi asibiti Inna asibitin da Daddy yake zuwa za muje?" inji direban. "EH can za mu je mana" suna isa asibitn aka dora ta abin tura marasa lafiya a ka shigar da ita wani daki. likitoci biyu suna tsaye akanta. Can suka fito inna ta mike da sauri ta tare su "Yaya likita? Yace, inna ki kwantar da hankalinki, damuwa ce ta yi mata yawa da bakin ciki, amma za ta samu sauki idan an ankiyaye dokokin da likita zai kafa mata. Yanzu mun ba ta gado an kwantar da ita.: A ka nunawa inna dakin da take ta shiga ta zauna a gefen gadon sannan ta zaro waya ta bawa me aikinta ta ce ta buga gidan Dady da gidan Aunty ta gaya musu. Cikin mintuna kadan 'yan gidansu duka sun zo har Dady da momy can gidan Aunty ma ta sako Haidar a gaba dole ya tuko motar suka zo. Gaba daya sun gewaye gadon da take kwance, kowa ya sa mata ido. Likita ya shigo ya zare ledar karin ruwan da ta ya sa mata wata. likita ya gaisa da Dady ya ce, dady sai an rinka kula da lafiyarta dole ne a rinka barin zuciyarta tana hutawa don a samu nutsuwa a rinka kiyaye duk wasu abubuwa ko maganganu da za su rinka bata mata rai a rinka yawan lallabata da rarrashinta har ta warke, idan ba haka ba tana gab da kamuwa da ciwon zuciya." Dady ya ce, "Ba komai likita insha Allahu za a kula kuma Allah ma zai kiyaye. Shin kuwa Haidar ya yi zukulu yana tunani a zuciyarsa ya ce, "Anya kuwa ba shi ya haddasawa jawahir wannan matsalar ba? shi fa musulmi ne ya kamata ya yarda da kaddara ko ba komai jawahir yar uwarsa ce yana da imani don haka ya tausaya mata halin da ya ganta a ciki. dazun nan ya gama gaya mata maganganu ga shi yanzu halin da take ciki. Dayan biyu ko rai ko mutuwa. Washegarin jikin jawahir ya yi sauki don tana iya komai da kanta wajen magariba Dady ya matsantawa likita sai ya sallami jawahidr sabo da gobe daurin aurenta Likita ya rubuta mata takardar sallama da magunguna Washegari aka daura auran Haidar da Jawahir, daurin auren da ya samu halattar manyan mutane da 'yan boko abokanansu haidar da yaya Abba da Nasir. Anyi taro lafiya an gama lafiya mata kuma sun shiga hadaniyar biki. Haka kawayen amarya suke ta shiga da fice na gudanar da hidimomin bikin kawarsu, amarya kuwa ba ta um bare um-um kowa kallon sa take yi. kakarta ta wajen uwa Hajiya Rabi ta zaunar da ita tana yi mata nasiha ki yi hakuri jawahir ki zauna a gidan mijinki lafiya ba ki da wani gata da ya wuce dakin mijinki. Ki rinka taka tsantsan da harshenki, kada ki gaya masa bakar magana ko wace za ta sa shi yayi fushi saboda lahirarki." kowa dai ya ta mata nasiha zai ce ta ji tsoron Allah ta yi biyayya ga mijinta. An gama biki amarya ta tare a tsantsareren gidan angonta da yake nasara G.R.A. Kowa ya fashe 'yan kawo amarya sun watse sai ita kadai kwal a cikin gidan sai maigadi da yake bakin get. Tana zaune tana tunanin irin zaman da za su yi da HAIDAR har bacci ya fara daukan ta a zaune ta ji an turo kofa anyi sallama an shigo. Ta yi saurin gyara zamanta . Ya shigo dakin ya nemi waje ya zauna ******SALON SO***** : ****PART 11 TO 15***** . BY SULAIMAN BOMBOY. . Ba ce mata komai ba ita ma ba ta kalli gun da yake ba. Can ya ce mata kinci abinci? "EH na ce. Ya janyo ledojin da ya shigo da su da karamar akwati ta siyen baki ya tura mata gabanta ya tashi ya fita. Jawahir ta yi tagumi a ranta ta ce, "O ni 'yansu, ga me so na can an kawo ni gidan wanda ba ya kauna ta ko da yake ni ma zan zauna ne darajar iyayenmu. "A nan ta tuno nasihar da mommynta ta yi mata. Jawahir ni dai babu abin da zan ce miki sai fatan Allah yayi miki albarka yanda kike binmu kike mana biyayya ubangiji ke ma ya baki 'ya 'yan da za su biki haka. Jawahir ta dauki duk abin daya same ki a rayuwa matsayin kaddara. ki kasance me biyayya ga mijinki ki boye sirrinku kada ki buda shi ga wani don Allah ya tsinewa matar da take bayyanar da sirrin mijinta. Duk abin da ya yi miki yi hakuri kada ki kai kararsa wajen kowa. Ki dage ki yi ta yi muku addu'a don Allah ne zai warware muku matsalarku. Ka bacin rai ya sa ki bin boka ko malam babu abin da za su yi miki face ki barnatar da kudadenki a banza kuma ki jawowa kanki tsinuwar Allah ki rike alkur'ani dan zancen Allah ne shi ne waraka ga komai. Jawahir ta saki ajiyar zuciya ta ce, "In Allah ya yarda zan rike nasihar mommyna. Haka ta kwanta ita kadai ga tsoro da yunwa tana jin amma ba ta bude ledojin da Haidar ya ajiye mata ba. Da asuba ta yi sallah ta dauki kur'ani ta karanta abin daya sauwaka ta yi addu'a ta ta sha fa ta cire hijabinta ta ajiye. Ta yi takumi, "Ni kuwa na je na hada break ko kuma na kyalle shi? Kai gwanda na yi ko ya ci ko ba ya ci Allah ya gani dai na fita falon tsarin falon ya yi mutukar burge ta da ba ta sha awa, lallai daddynta ya kashe mata kudi. Ta bude kicin din shiga haduwarsa ya yi mugun gigita ta, sak irin wanda a ke nuno tallolinsu ne kasashen waje, duk wata na ura ta amfanin dan Adam don hada abu a saukake an tanadar mata a kicin din nan, sannan duk wani kayan girki da za su bukata an tanade shi ta bude disk freezer cike yake da kaji, zabi xuwa naman kasuwa duka danyu, sai daya firizar kayan miya ne irinsu attarihu tattasai, tumatir, albasa, koren, wake, karas, kabeji da sauransu. Firinjin tsaye kuwa lemummuka ne kala kala na kwali da na gwangwani da robobin ruwan sha, kamar su swan water, Highland water, da dai sauransu. Ta ga wata kofa daban a kicin din ta bude ta ta shiga ashe sito ne kalolin abinci iri iri buhunan shinkafa, katon dinsu taliya, makaroni, kuskus, buhun sikari da na fulawa, garwar manja da na jan kuli da kuma man shanu, busasshen kifi, daddawa, kanwa busasshiyar kubewa, magi kama daga Reko, onga, kori, Ajino-moto da dai sauransu, babu abin da za ta nema na amfani komai an dire mata.: Ta debo dankali ta fere ta soya ta jona ruwan zafi ta sa citta da kanun fari, ta zuba ganyen shayi me kamshin Nescafe ta koma daki ta dauko ledar jiya gasassun kaji ne manya guda uku ta zuba su a oben ta dumama su. Ta fasa kwai ta soya ta debo filas-filas masu kyau 'yan dubai ta zuba komai a ciki ta rufe ta juye ruwan shayin a fulas din shayi wanda yake duk saiti ne da fulas din da ta zuba ragowar kayan a ciki. Ta jere komai a tebir ta debo kofuna da filet da cokula duk ta zube kan tebir din ta sa wani farin kyalle me ban sha awa ta rufe kayan kan tebir din. Ta dauki nata break din ta yi dakinta da shi. Ta rufe kofarta ta shiga toilet ta yi brush sannan ta ci ta koshi ta koma gado ta kwanta. Mintina kadan bacci ya yi awon gaba da ita. Shikuwa Haidar da ya tashi da asuba ya yi sallah ya yi karatu ya shafa addu'a gado ya koma ya kwanta saboda baccin gajiya da yake ta dawainiya da shi. Karfe tara ya tashi na safe ya yi mika tare da salati ya duro daga gadon ya nufi toilet. Ya salla wanka ya zo ya gama goge gogensa da shafe shafensa ya yi tsantsararriyar shiga, shiga ta alfarma ya feshe jikinsa da turaruka. A zuciyarsa yake cewa ya kamata na je na gano yanda yarinyar nan ta tashi ko don nasihar da Abbansa ya yi masa kamar haka....... "To Haidar yau Allah ya nufa an daura auernka da jawahir to duk wani nauyi da hakkinta ya koma kanka, amana ce a gare ka, idan ka zalince ta ko ka cutar da ita kai da Allah, idan ta yi maka abin da be yi maka dadi ba ka zaunar da ita ka nusar da ita cikin nasiha da tattausar murya. Kar ganin yanzu ta zama ikonka tana zaune a karkashinka wallahi idan ka zalince ta ubangiji ba zai taba kyale ka ba, sai ya fitar mata da hakkinta don haka ka kiyaye." Ajiyar zuciya Haidar yayi, "Haka kawai a daure ka da jijiyar jikinka, bari na je na gani ko ta karya. Ya sauka kasa da yake benen nasa a cikin falonta yake. Ya kula da tebir din da ya sha kwalliya da kayan alatu. Ya karasa wajen ya yaye farin kyallen ya bude komai. Kamshi ya daki hancinsa nan da nan sha awar abincin ta kamashi. Ya zauna ya hada ruwan tea me kauri ya debi soyayyen dankali da kwai da kaza daya. Haidar ya rinka ci yana lodawa cikinsa don jiya da daddare bai ci komai ba ya kwanta, yanzu kuwa ai ya yi lodi, ya yi gyatsa tare da yiwa Allah godiya. Ya mike ya nufi kofar dakin jawahir ya ji ta a rufe. Ya samu takarda da biro ya rubuta mata sako kamar haka: "idan kin tashi ki yi break ni mun fita gaisuwar surukai sai yamma zan dawo." Haidar Ya ninke ya dora kan tebir din. Ya fice. Ya samu abokanansa suna jiransa suka tafi gaisuwar surukai. jawahir sai sha biyu na rana ta farka, tana mikewa ta fada toilet ta yi wanka ta kammala shirinta sannan ta fito falo, ga mamakinta ta ga Haidar ya ci break din da ta shirya masa. Ta hango takarda ta dauka ta bude ta karanta ta tabe baki, "Kada ma ya dawo ni ko kwana zai yi me ya dame ni?" Ta dauko yogougt ta zauna tana yagar kazar tana korawa da nonon har ta koshi. Wajen sha biyu da rabi direba ya kawo Inna da kannanta Auwal da sani da su Hassana da Usaina kannan Haidar. Jawahir ta cukuikuye inna tana tsallen murna. Inna ta dube ta tana dariya ta ce, "Ke cika ni kada ki karasa ni, ni ina can zuciyata ta kasa sukuni sabo da tunanin yaya kwana ke kuma kina kokarin karasa ni. jawahir ta yi dariya, "Amma dai inna a nan za ku kwana ko?" Inna ta tabe fuska ta ce, "Ke ba na son hauka yanzun nan ma za mu juya. Hassana ta ce, "Allah Aunty ni dai gidanki ya ba ni sha awa zan kwana. Usaina ta ce, "Lallai kina so Yaya haidar ya yi tamaula dake kenan.? Jawahir ta ce, ba wani abu da zai yi mata kin ji Usainar nan wai don kar ta kwana, ba abin zai yi miki Hassana." Inna ta ce, "Babu wanda zan bari, kafata kafarsu. Auwal ya ce, "Su Aunty jawahir 'yan gayu. "Gaba daya sukai yi dariya. Sani dauko muku ragowar break din Yaya ku ci. Ta tashi ta shiga kicin ta kwaso musu yogouht da lemummuka da ruwan sanyi ta zube musu. Da ragowar gasassun kajin amarcinta. Inna ta gyara zama da jikokinta suka ci suka koshi. Inna ta kara yi mata fada da nasiha. Karfe hudu suka tafi. Jawahir ta mike ta yi sallah bayan ta idar ta shiga kicin ta dauki kaza daya ta yayyanka ta yanka albasa ta sa gishiri da citta da magi ta dora kan wuta. Ta debi kayanmiya yanda zai wadace ta ta markada ta dora ruwan kuskus. Ta gama hada soyayyiyar miyarta ta dafa kuskus dinta da ya sha karas da koren wake ya yi wara wara da shi gwanin kyau. Ta gasa kifi irin manyan nan ta yi farfesun kayan ciki, ta markade kwa kwa a ciki blinder ta tace ta sa madara, filebo, sukari ta hada lemo me dan karen dadi. Ta samu wasu kayatattun fulas ba irin na safe ba ta kuma jere komai a kai. Ta hau saman dakin nasa, ga mamakinta sai ta gan shi a bude ta gyara masa gadon da ya kwanta ta kade komai ta share masa dakin. Ta wanke bandaki ta goge ta kunna turarukan wuta ta fesa Air freeshner a kowacce kusurwa, ta sakar masa A.C Nan da nan sanyin dadi ya soma tashi. Ta rufo masa dakin ta sauko ta gyara falon kasa da nata dakin ko ina ta feshe shi da Air freshner da turaren wuta dan maiduguri ta saki labulayen ta kunna A.C ta rufe kofar falon ta shige dakinta ta rufe ta fada toilet don yin wanka Sai karfe biyar da rabi Haidar ya dawo gidan a gajiye ga yunwa da take azalzalassa don tun break din da ya yi bai sake cinn wani abun ba. Don shi Allah ya yi shi mutum ne mai kyankyami ba ko ina yake iya cin abinci ba. Megadi ya wangame masa get din ya shigo ya rissina ya yi masa barka da zuwa. Ya murda kofar falon ya shiga tare da yin sallama shiru kamar ba kowa a gidan. Daddadan kamshi ya bugi hancinsa, ko ina tsaf a share a goge ya ji gyara, ya yi sha awar yanda take da tsafta take kula da komai. Ya haye samansa yana tura kofar dakin, nan ma sanyin da kamshin dadi suka yi masa sallama. Ya sheka ya limshe ido ya yi godiya ga Allah, shi kansa falon saman nasa ta canja masa tsarin gyara wanda kuma hakan ya fi kyau yana shiga cikin dakin nasa sai kansa ya kwance, wani hadadden zanin gado ta shimfida masa , ai yanda ta dame gadon ya burge shi ya cire kayansa ya fada toitel ya fara wanka.Ya gama shirinsa ya sa kananan kaya. Sun karbe shi kuwa sun yi masa kyau. [07069210827: Ya feshe jikinsa da turaruka ya sauko kasa ya hau tebir ya bude komai, kamshin girkin ya buge shi sha awa da jin dadi suka bige shi. Ya zauna ya rinka dibar garar girki, yana ci komai na kan tebir din sai da ya ci da ya wa ya ci ya koshi ya yi hamdala ga ubangiji. Ya rinka tsiyayar lemon kwa kwar nan yana sha, don Allah daman hausawanmu sun iya hadadden lemo haka, amma muke bugewa kullum yawon siyen juice. Ya cika kofin tangaran da shi ya tashi ya koma kan kushin can gefe daya ya dauki jarida yana karantawa yana kurbar lemon kwakwar. Ita kuwa jawahir tana daki ba ta ma san ya dawo ba ta gama shirya kwalliyarta cikin riga da siket na atamfa kwali wax, rigar fitet ce 'yar firit,siket din ya yi tsantsan a jikinta. Ta dora daurin dan kwali wuyanta da kunnanta wani rantsattse fashion ne mai kyau. Ta feshe ilahirin jikinta da daddadan turaruka masu kamshi. Ta bude kofar dakinta ta fito kamshin da ya ji ne ya sa shi dago kai ya kalle ta, a ransa ya fada, "Yarinyar tana da kyau sai ka ce Aljana, ga shi ta iya gyran jikinta. Yanda siket din ya matse ta dole ta rinka takawa sannu a hankali gudun kada ta harde. Ta shiga kicin ta debo abinci a filet dan kadan sai ka ce wadda za tabawa dan yaye sai robar nono yogougt dake daya hannun nata. Ta zo ta nutse a cikin kujera ta dauki remote ta kunna T V. tashar CNN ta kunno, sannan ta fara cin abincin, yanda take diban abincin kamar ba ta son ci a yangance. Duk abin da take yi idon Haidar yana kanta, ita kuwa ba ta san ma ya dawo ba bare ta san yana falon. A zuciyarsa ya ce, "Yaushe dama za ta girma tana cin wannan dan mitsitsin abincin kamar na 'yar yaye. Can wayarta ta yi kara ta dauka, tana dubawa da murnarta ta dora a kunnanta, "Hello Dadyna. sai ta kunna (Handsfree) Daddy ya ce, "Jawahir yaya kike? Ya megidan naki? "Wallahi lafiya lau Dady muna zaune kalau. "Kina son masu aiki ne a kawo miki? Cikin shagwaba ta ce, "Lah Dady mai aiki, ni wallahi ba na son kowa su zo su yi batawa mutane waje. don iya girkinmu mu biyu da gyaran dakunanmu Dady ai duk zan iya. "To jawahir wanke-wanke fa, ga sharar harbar gidanku.? Dady ka san ba na son kazanta da gama girki nake wanke kayan na goge su na mayar inda suke. Harabar gidan kuma dakin saukar baki yana da yaro da yake gyara masa me bawa fulawowiyin gidan ruwa. "To jawahir wa zai rinka ba su abinci ko har da su za ki yi rinka yin girkin? Ta kara shagwabewa, "Uhm Dady wallahi ba zan yi musu girki ba, abincina daga ni sai Yaya kawai. "To shi ke nan jawahir za a samu haidar din na yi mishi magana na ji yanda za a rinka yi da su wajen ba su abinci." Cikin shagwaba ta ce, "Don Allah Dady kada ka yi masa magana ya zo ya ce sai na rinka girkin da su ka ga wahala zan sha. "To jawahir ai a karkashinku suke, dole ku rinka kula da hakkinsu ko to kwace kuma za ku bar su da yunwa. Cikin shagwaba ta ce, "Haba Dad. to Dady na yarda a kawo tsohuwa amma ba za ta rinka shigo min sashena ba, sai dai ta tsaya can bangaren masu aiki ta rinka da fa musu abincin, ai ya yi ko Daddy.?" "Yauwa ko ke fa jawahir gobe za a kawo ta, Ki kara hakuri jawahir ki dinga biyayya ga mijinki. Allah ya yi muku albarka . To Dad na gode, "good day Dad." Tayi ajiye wayar ta mike ta dau filet din ta shiga kicin. Haidar ya mike ya haura samansa ya yi dai dai a gadonsa yana tunanin hirar jawahir da Daddynta. A ransa yake cewa, "Ko dai don muna 'yan uwa ne halayyarmu da ra'ayinmu suke neman zama daya? Gaskiya ta burgeni da za ta rinka yi min komai da kanta, don ni na tsani gidan da me aiki take yi wa matar gidan da mijinta girki, amma jawahir tana da dadin murya ga dadin saurare, ban so suka gama hirar ta su ba. To haka da i zaman ya ci gaba tsakanin miskilan guda biyu. kowanne yana ji da girman kai da miskilanci babu wanda zai wa dan uwansa magana idan har sun hadu da safe za ta ce masa ina kwana. Yayin da shi kuma yake daukan lokaci kafin ya amsa da lafiya lau. To sai ta yi shigewarta daki ba ta fitowa har sai ya tafi. sannan ta zo ta gyara musu dakunansu ta turare da turaren wuta ta feshe ko ina da Air freshner ta zauna ta shirya musu hadadden girki me gamsarwa. Ta hada masa lemo da kanta kullum da sabon samfir din girki da lemon da take yi masa. Ba ta taba barin waje da datti ko kura ko ina fes a gyare dai dai da wanke kwanikanta ita take yin abinta. Ta gyara kicin dinta fes kamar ba a yi komai a ciki ba. Tukwane ne kawai da kaskon suya saboda maiko take bawa Dela me aikinta ta wanke mata Tun da akawo Dela take zaune a bangaren masu aiki za ta yi girkinsu su uku da maigadi da ita sai yaron gidan da ta yi gama za ta wanke komai ta share ta goge da yake ita ma me tsafta ce shi ya sa suke shiri da jawahir din. Haidar kuwa yana jin dadin yanda jawahir take da tsafta komai take kulawa da shi yanda ya kamata, don haka duk san da ya taso daga office burinsa ya yi sauri ya dawo gida don ya narki special din girki da jawahir za ta yi masa. Ya zauna a kayataccen falonsu yana shakar daddadan kamshin falon. Idan ya tashi daga office yana biyawa ta gidansu a gurguje yake yin komai don yana sauri ya koma gida. Idan Aunty ta ce masa ga abinci ya kan ce um Aunty sai na je gida zan ci. Duk da ba magana suke yi wa junansu ba, to amma hakan bai hana su kyautatawa junansu ba Ana yawan kawo mata kannanta Auwal da Sani da kannan Haidar Hassana da Usaina idan yamma ta yi direba ya mayar da su gida Yaya Abba ma da yaya Nasir suna yawan zuwar mata. Inna ma ta na kan zo amma ba sosai ba iyayensu ne dai har yau ba su zo ba. HAIDAR ya samu kwanciyar hankali don ba a bin da ya ke damunsa don haka jikinsa ya kara murjewa kyansa ya kara daduwa kowa ya kalli fatarsa ya san ta goge da jin dadin duniya ita kuwa jawahir da yake abincin be da meta ba to yanda take haka take babu wata 'yar kiba da ta yi. Shekara daya ke nan da yin auren har yau jawahir ba ta taba lekawa kofar gida ba. Yau asabar da jawahir ta kammala da hada break dinta ta diba ta ci ta gama gyara wajen ta sa turaren wuta ta feshe da gidan ta shige toilet ta yi wanka. Yau shigar turawa tayi 'yar bingilar shimi ta saka iya cibiya me siririn hannu sai dogon wando da ya dame mata cinyoyi da kafar wandon an bude shi ta hade gashinta a tsakiyar kai ta sa tafkeken ribon ta daure shi. Cikinta a dame kamar ba ta zuba masa abinci ba, fuskar nan tata sai fitar da sheki da wa ni asirtaccen kyau ta ke yi, ta gama feshe jikinta da tuararuka ta fito falon inda Haidar ya ke break ta durkusa ta ce, "Ina kwana?" bai juyo ya kalleta ba ya ce, "Lafiya lau. Ta mike ta isa bakinTV ta dauki takarda da biro ta koma ckin kujera zaman mutu daya ta kwanta tana rubutu. Tun da ta mike Haidar yake bin ta da kallo sai hadiyar yawu kawai yake yi ta yi mugun ba shi sha awa, hankalinsa ya tashi sosai. Ta gama rubutu a takardar ta ninke ta taso cikin nutsuwa ta zo gaban Haidar ta ajiye masa a kan tebir dinta ta juya ta koma daki, shi kuma ya bi ta da kallo. Sai da tashige daki sannan ya ware takardar ya fara karantawa . Yaya Don Allah yaya ina so zan je gidanmu da gidan inna da wajen Aunty. Ina so na taho da sayyid Autan Aunty idan ka yarda. Jawahir Yana gama karantawa ya ajiye ya ci gaba da yin break dinsa sai da ya gama sannan ya mike ya dauko takarda da biro shima ya rubuta mata kamar haka. "In kin shirya ki jira ni na kai ki da kaina, Sayyid kuma in kin ga ba zai takura miki ba kya iya daukoshi Haidar Jawahir duk ta matsu da ta ga amsar da zai ba ta. don ita dai tana so yau ta je gidajen nan ko dan dadewar da ta yi rabonta da fita . Ita jin kanta da miskilancinta ya hana ta ta fito bare ta ga amsar da ya rubuta mata , shi kuma girman kansa da isarsa ba za su bar shi ya kai mata ba. Sai da ya gama kallon sa da hutawarsa sannan ya koma sama. Sai da ta ji tafiyarsa ta fito ta dauki takardar ta karanta, aikuwa sai ta hau tsalle tana murna kamar yarinya. Nan da nan ta shiga shiri a kakale nan a kakale can ko ina ta yi fes kamar wacce aka karawa kyau. Wani dandasheshen less ta saka me dan banzan kyau da shegiyar tsada. Ta yi kyau kamar ka sace ta ka gudu don haduwar da ta yi. Ta kalminta da mayafinta da jakarta duk ruwan less din ne. Takalmin me tsinin dunduniya. ta hakimce a falon tana jiran futowarsa megidan Ba ta jima ba sosai ya fito cikin shiga ta wani danyen boyal baki sai sheki yake yi, hular kansa baka mai gashi, takalminsa baki sai agogon hannunsa na Daimond. Duk sun yi kyau kamar wadanda za su zaben sarauniyar kyau. Ya yi waje ba tare da ya kalle ta ba, ta mike ta rurrufe ko ina ta fito tana takawa sannu a hankali yana kallon ta ta mudubin motar, duk sha awarta ta motsa shi, amma saboda iya jan ajinsa ba zai taba nuna mata ba, ko ya bari ta gane ba. Ta kama murfin mota ta bude ta shiga baya ta zauna, be kalle ta ba kuma be yi mata magana ba be kuma ja motar ba. Ya yagi takarda ya yi rubutu ya cilla mata baya ta dauka ta duba, "Ba ki kai matsayin da zan zama direbanki ba, "Tana gama karantawa ta bude ta fito ta dawo gaban motar ta rufe. Ya kuwa figi motar a guje kamar me shirin tashi sama. Babu wanda ya yi wa kowa magana haka suke tafe sai da suka zo wani super market ya fita ya yo musu tsaraba suka ci gaba da tafiya. Gidansu ya fara kai ta, yana tsayawa ya mika mata takarda ta duba ta karanta a wa daya na baki ki yi ki fito mu tafi. Ba ta ce komai ba ta bude ta fita ta yi sallama falon ta shiga. Aunty tana ganinta ta mike ta taro ta da murna tana jawahir 'yata barka da zuwa 'yata ta kaina." Ta rungumeta ta a jikinta, "Zo mu hau sama Alhaji ya ganki tukunna, "Suka hau ta durkusa har kasa ta gaida Abba cikin fara'a da murna yake amsawa, "Jawahir ke ce haka? lallai yau zan huta da mitar Auntynki." Aunty ta ce, "Wa ya kawo ki ne? ko kun dauki direba ne? Cikin jin kunya ta ce, "Ai yaya ne ya kawo ni. Tana rufe baki ya yi sallama ya shigo kai tsaye ya wuce gaban Abbansu ya zauna ya gaishe su. Abba ya dafa kan Haidar ya ce, "Yau na ga jawahir na gode muku da yanda kuka rike kanku ba ku mu kunya ba. Haidar ya ce, Yanzu ma cewa ta yi na kawo ta za ta dauki Sayyid ga shi ban gan shi ba. Aunty ta ce, jawahir ta Sayyid ai yanzu ba irin da ba ce da kike zuwa ki dauke shi ya yi kwana da kwanaki a gidanku yanzu ai sai ya takuraki. Cikin jin kunya ta ce, "Lah Aunty wallahi ba komai ai ba zai takura ni ba. To shikenan gobe za a kawo miki shi ya yi kwana biyu kawai. Ta ce, to Aunty na gode. Aunty da kanta ta kawo musu abubuwan ci da sha suka sauko kasa da Aunty. Duk yanda Aunty ta yi don ta ji ko da wani abu a tsakaninsu amma jawahir ta ce kalau suke. Haidar ya shigo ya yi wa Aunty sallama ya fita jawahir ta kalli agogon hannunta ta ga awa dayan da ya ba ta saura minti uku ta mike ta ce Aunty zamu tafi. "Haba jawahir tun yanzu? Ta ce, Ai za mu bi ta gidanmu da gidan inna. "To jawahir na gode Allah ya yi muku albarka. Manya ledoji biyu Aunty ta ciko mata da kayayyaki. Abba kuma ya ba ta dubu ishirin. Daman Haidar ya sa maigadi ya shigo musu da tsarabarsu. Ta bude motar ta shiga awa dayan ta cika dai-dai shi ma ya shigo suka tafi. Gidan Inna ya kai ta shi ma sai da ya ba ta takarda ta karanta kar ki wuce awa daya. Ta shiga gidan inna murnarta da tsallenta ta cukuikuye inna. Inna ma murna take yi ta zaunar da ita "Daga ina haka? ke me Haidar din yake baki kika sake zama baturiya haka sai dai rashin kiba amma kin kara kyau ko dai ciki ne dake? Daidai shigowar Haidar a zuciyarsa ya ce, "Ciki yaya za ayi ayi ciki yanzu ai ta yi kankanta. Ya yi sallama falon ya shiga inna ta tare shi da murna duk bakinta yaki rufuwa ganin jikokinta shar dasu babu wata alamar damuwa a tare da su. Inna jikinta sai rawa yake yi ta rasa inda za ta sa kanta don murna, ta kawo musu wancan ta kawo musu wannan tana ta hira. "Dan ka'ida bature ya duba agogo saura minti biyu awa daya ta cika Haidar ya yi wa Inna salllam ta rinka yi masa godiyar wannan uwar tsarabar da suka kawo mata. Ya fita ya koma mota yana jiranta. Sai hira kuma ta dawo sabuwa tsakanin inna da jawahir har ta manta da dan ka'ida lokacin da ya ba ta, to tana ta shan labarai da abubuwan ban dariya daga inna. Ba ta yi aune ba ta ga kara minti arba'in da biye a kan awa dayan da ya ba ta zumbur ta yi ta mike inna za mu tafi sai kin zo. Inna ta ce, Au ba sai magariba za ku tafi ba? "Ta ce, "Uhm yana mota yana jira na. "To shi ke nan na gode ku gaida gida. Allah ya yi muku albarka. A cikin mota ta same shi ya kwantar da kujera ya na shan A.C da sautin rediyo ya lumshe ido kamar mai bacci. Ta bude mota ta shiga ta zauna. Ta fi minti goma ba shi da niyyar ta shi bare ya tuka motar su tafi. Ta gaji da jira ta ce, "Yaya na fito. Ya bude ido daya ya ce, Awa nawa na baki.? Ta ce, "Awa daya." "Sai yanxu awa dayan ta cika.? "A'a Inna ce ta tsayar da ni da hira." "To kin cinye lokacin da za ki yi a gidanku, yanzu gida za mu tafi sai wani lokacin kuma." Gabanta ya fadi, duk da dokin da take yi na zuwa gidansu ga shi ta fito din amma ba damar zuwa gidan nasu. Ita girman kanta ba zai bar ta ta ba shi hakuri ba bare ya hakura yakai ta. Kawai sai ta ji hawaye yana zubo mata. Haidar na kula da ita amma sai ya dauke kansa ya ci gaba da tukinsa kamar be san tana yi ba. Tana kukanta har da shassheka amma sai ya karo rediyon ma don kada yaji kukan. Ba wanda ya sake cewa da kowa komai har suka je gida Yana tsayar da motar ta bude ta fito tana goge ido ta bubbude ta shiga dakinta ta fada gado ta yi rub da ciki ta ci kukanta ta koshi. Ta shiga ban daki tayi alwalla ta yi sallar la'asar zuciyarta tana ta zuga ta da kada ta yi masa girki don ya dan dani bacin ran da ta ji, to kuma sai ta yi wani tunani ai ita ta fara bata masa kuma girman kai ya hana ta neman afuwarsa to idan ba ta yi masa girki ba ai ta dada shiga hakkinsa kuma ita ba iya cewa za ta yi ya yi hakuri ba, kuma zai yi bacin ran da ya fi nata, ita kuma ba burinta ke nan ba. Duk da irin zaman da suke yi na rashin yiwa juna magana to amma ba ta so ko kadan ta ga ta bata masa rai. shi yasa kullum take yin abin da ta san zai ji dadi. Ta mike ta fito falo takarda ta gani a ninke, "Na fita unguwa sai magariba zan dawo," Ta yaga takardar ta fada kicin ta dora girki . Yau tuwon samovita ta yi miyar danyan kubewa da ta burge kaza a ciki. Sai ta gasa masa dan shila ta soya masa kifi ta hada masa lemon abarba ta jere komai a tebir. Yau Dela ta bawa wanke wanken don zuciyarta a bace take. Kafin ya dawo ta gama abin da take yi ta gyara wajen ta shige dakinta ta kulle kofa. Sai da ya yi sallar magariba sannan ya shig, ga mamakinsa sai ya ga tayi abinci a zatonsa yanda ya bata mata ba za ta yi girkin ba, har yana shirin fita Hotel ya siyo musu. Duk kuma sai ya ji tausayinta ya dame shi a ransa sai ya yi da yasanin bai ki kai ta gidan nasu ba. Ya zauna ya ci abincinsa ya koshi yau har da senti ya mike ya je ya sake alwalla ya yi sallar isha'i. Haka ya yi zaman falon har goma na dare amma bai ga fitowar ta ba, abun ya dame shi dan be ji dadin yanda ta takura kanta ba. Haka tai ya hakura ya je ya kwanta zuciyarsa ta na ta tunane tunane. "Washegari da safe da ta gama komai da ya shafe ta ta daddasa kwalliyarta yadda ta saba ta fito yana tebir yana break ta durkusa ta ce, "Ina kwana.?" Ya amsa, "Lafiya lau jawahir kin kwana kalau.?" "Lafiya kalu." Ta ce ta mike tana koma daki tana mamakin canjin yau da ta samu na sakin fuskar Haidar. Har ya fadi sunanta ba tare da ya ce mata kwaila ko tatsitsiya ba. ******* ******** ****** ******** Haidar bai dade ta fita ba direba ya kawo Sayyid, jawahir ta yi murna da farin cikin ganin sayyid don ta samu abokin debe kewa. Sai magariba Haidar ya dawo sayyid yana jin karar motarsa ya fito a guje ya tarye shi, Haidar ya dauke shi ya rungume shi, "Auta wa ya kawo ka? ina ka baro Auntyn taka? "Tana gida Abba ya ce kada na dade kwana biyu zan yi." Haidar duk ya gama wani abu da zai yi na game da cin abinci, wanka ya sa kananan kaya na shan iska ya haye saman gado yana shan surutun Sayyid da yake ba shi dariya. Wayarsa ta fara ruri alamar ana kiransa. Haidar ya duba ya ga bai san lambarba ya share ya ki dauka, ta katse dan kanta, can aka sake bugowa be dauka ba ta kuma katsewa. Sai da aka yi sau biyar a na shi dan Haidar ya gaji ya dauka, "HELLO. Ya amsa a kasan makogaronsa. Cikin doki Kausar ta amsa, "Ranka ya dade saraki har yazu mulkin yana nan ne ba a sauke ba?" Ya ce, "Wake magana ne? ko sai na ajiye kan wayar ne.? Ta ce, "A'A ayi hakuri Saraki kausar ce. Yac, "Wa cece kuma me wannan sunan.? "Ranka ya dade Saraki Kausar dinka da kuka yi karatu America tare ka gudo ka bar ta. "Oh. Kausar kenan kin cika na ci, yanzu sai da kika lalubo ni." "To ya zan yi Haidar wallahi tun ranar da ka taho ban kuma nutsuwa a zuciyata ba sai yau da na ji muryarka. Haidar ciwon son ka ya zamo gyambo a cikin zuciyata. Haidar ni musulma ce ka tallafi rayuwata Haidar ka zo gare ni ka aure ni. "Haba Haidar ka san darajar 'ya mace da kimarta amma duk na watsar na tunkare ka na ba da kai na ke rokonka da ka aure ni. Haidar wace irin zuciya ce da kai? Ka tuna fa kana da kanne mata kuma nan gaba in Allah ya ba ka haihuwa kila ka samu 'ya 'ya mata, to ya za ka ji yayin da 'yarka ko kanwarka ta fada irin wannan halin da na fa da akan kan wani? Ka san kaddarar ubangiji babu inda ba ta fadawa mutum." Haidar ya ce, Ki yi hakuri ba burina na yi miki wulakanci ba, ai duk inda masoyinka yake ya fi makiyinka sau dubu, to amma kin ga yau shekara daya ke nan iyayena sun hada ni aure da wata 'yar karamar kanwata, wadda har a yanzu da nan gaba rainonta nake yi." Kausar ta ce, Haidar don Allah don Annabi ka amincewa bukatata wallahi ni ba ruwana da wata matarka don ba a kanta zan zauna ba. Ya ce, "To shi kenan Kausar ki ba ni lokaci zan yi shawara. Ta ce, "Haba Haidar. Ya ce, "Uhm no kada ki damu ba matsala insha Allahu komai zai zo da sauki. Suka yi sallama kowa ya dire wayar. Haidar ya fada tunani ko na amince da bukatar Kausar na aure ta, ko ni ma na ji yanda auren yake? To ya zan yi da Aunty da Abba? ko da yake in sha Allahu ba za su zamo matsala ba. Haba dai ya kwanta yana sake- saken abinyi. Washegari yana office wajen azahar jawahir ta yi baki kawayenta ne suka zo. An sha hira kuwa inda jawahir take cewa, "Bilki ai kun yi min rashin mutunci wai duk yanda muke da ku aure shekara daya amma kuka kasa leko ni." "To ai kin san abun ne sannan ba kwa shiri da shi mu zo wani abun ya faru sai ya zamo matsala, some kin ga yanzu ai komai normal don yanda kike wannan kyallin goshin na san an samu rabo ma ( Hahaha kunji gulma. Hmmm Ni dai Bomboy ba ruwa na idan Haidar yaji ku). Ta yi dariya, "Uhm kwa ji da shakiyancinku ku zo mu ci abinci." Wajen karfe hudu suka gama shirinsu suka fito za su tafi ta yo musu rakiya har bakin get, megadi yana dan dakinsa yana lazimi, Hira suke yi suna tafawa tare da shewa da dariya. Sai ga motar Haidar ya. [8:35PM, 12/6/2016] : shigo ya danna hon megadi ya taso da sauri ya bude masa get. Haidar ya hango jawahir ba mayafi a jikinta ta yi kwalliya tana ta faman dariya duk sai ya ji kishi da bakin ciki ya dame shi. Yaya za ayi ma ta fito nan a haka? Ga megadi da 'yan aikin gida suna nan du su gano ta. Lallai ma yarinyar nan. Ya yi parking ya fito gunsu ya nufa kawayenta suka gaishe shi ya kalli jawahir ke me ya fito dake nan? Wa ya ba ki izinin zuwa kofar gida.? Kanta a kasa ta ce, "Kawayena ne suka zo shi ne na rako su. Rakiya ba ta isa ba iya kofar cikin gida har sai kin fito bakin get.? Ya shige ciki ya bar ta a nan. Kawayenta suka ce, "Lallai Haidar yanzu har wani kishinki yake? "To Allah ya sa dai mu jawo miki wata matsalar ba.?" Ta ce, "Haba dai ba komai ai yana da saukin kai shi ke nan kuma fadan ya wuce. "To mu dai mun tafi sai wata rana." Suka fita ta juyo ta shigo cikin gidan. Yana zaune a falo ta tafi za ta shige daki ya ce, "Ke zo nan. Ta dawo ta durkusa nesa da shi. "Daman in ba na nan bain da kike yi ke nan ko? Kalle ki yanda kika fita ga megadi da yaran gida duk suna ganin ki ko kin manta cewar ke matar aure ce? To bari ki ji duk da an aura min ke ba tare da ina son ki ba, to hakan ba zai hana ni yin kishinki ba, kuma dole ne na sa miki ido don ganin yanda kike tafiyar da rayuwarki, kada na kara ganin wata kawa ta zo miki kin ba ta fuska bare su zo su bata miki tarbiya ko su rinka zuwa tsegumi su samu damar bugun cikinki kina gaya musu sirrinki ko? Ita dai ba ta ce koami ba ya karaci fadansa ta tashi ta yi shigewarta daki. Tana barin wajen wayar Kausar ta shigo, "Hello Kausar kina lafiya.? "Lafiya lau Haidar shiru banji ka ba. Ya ce, "Kai kausar kin fiya gaggawa, amma ki ba ni adres din gidanku insha Allahu jibi zan zo, ta saki wani ihun murna yayin da take gaya masa adres din gidansu dake Abuja. Suka yi sallama ya ajiye wayar. Washegari yana zaune a office ya kifa kansa da tebir tunanin yanda zai bulluwa da iyayensa maganar Kausar yake yi. Abokinsa ne ya shigo ya sa me shi a haka. Duk sallamar da yayi bai ji shi ba bare ya amsa masa. Faruk ya kwankwasa masa tebir din gabansa. Haidar ya yi firgigit ya dago kansa ya kalli Faruk din ya saki ajiyar zuciya. Ya ce, "Yaushe ka shigo ban ji shigowarka ba.? Faruk ya ce, "Yaushe dama za ka ji ka tafi cikin wannan zurfaffan tunani haka, wai don Allah me yake damunka ne? jiya da yau duk wani sukoko nake ganin ka. Ya ce, "Ga ni nan dai abubuwan ne suka tarar min "Ba dai matsalar jawahir ba, ca nake mun gama wannan maganar da kai. Haidar ya ce, "Ai ni ba zan taba iya abun da ka ce na yi ba. Ciknin zaro ido ya ce, "Ba dai kana nufin har yanzu babu abun da ya hada ku ba?. Aure shekara daya. "To kai me kake tunanin zai faru? kanwata ce fa. yarinya ce, ko hannunta na kama ai raina ni za ta yi." Faruk ya ce, "Amma wallahi kana daukan alhakinku. Gaskiya ba ka kyauta ba, yaya za ka rinka wahalar da yarinya, kana zaton dutse ce ita ko waliya ce da ba za ta ji sha awa ba? Haidar ya ce, "Ko dai take wahalar da ni tana gasa ni, ka ga dai ni nake gaba da ita ya kamata ta fara neman sulhu da ni, to amma yarinyar nan gaisuwa ce kawai da safe take hada mu. Ga yarinyar ta iya tsara kwalliya komai ta sa sai yayi mata kyau ya yi das a jikinta kamar Aljana. Duk dare yanzu bacci gagarata yake yi, na dinga murkususu ke nan ina juyi sai ka ce dole, ai ba waliyyi ne ni ba, don haka na yanke shawarar aure zan kara a kwanan nan. Faruk ya dafe kirji ya ce, "Aure Haidar! kai kuwa me yayi maka zafi? Ba gwanda ka nemi sulhu da matarka ku dai daita ba. : (Hmmm barshi da kanshi zai sauke wannan jiji-da- kan. Mu dai yan kallo ne kuma yan rahoto. Da fatan dai idan anzo kamen dan leken asiri ba zaku nuna ni ba). ((((((((((SALON SO))))))) (((((PART 16 TO 18))))) : BY SULAIMAN BOMBOY. . Haba Faruk yaya za a yi na kwantarwa da wannan karamar yarinyar kai. shi kenan na ba da kaina girma kuma ya fadi, ni dai kawai aure zan yi na rabu da ita ta karaci tsiyarta ita kadai. Faruk ya daure fuska alamar ba wasa ya ce, "To kai duk abun da ake gaya maka ba za ka ji ba ko, to shi kenan ka je ka aika ta abun daka ga dama, in kuma abu ya kwabe maka kada ka sake ka nemeni tun da ban isa na ba ka shawara ka dauka ba, "Faruk ya juya ya fice tare da bugo kofar. Haidar ya yi ajiyar zuciya tare da tallefe kansa da hannu biyu, "Gaskiya ba na jin zan iya fasa auren nan, ni kawai zan yi auren nan ne don debewa kaina kewa da sha awa saboda kullum ni na san yanda nake kwana ina cutuwa. To me yayi zafi ni dai ba zan kai kaina ga halaka ba bare na nemi matan banza Allah ya kiyaye mu da aikata zina gwara kawai na yi auren, "Haka dai ranar ya wuni babu wata walwala. Alhaji Sa'adu mashi, babban ma'aikacin gwamnati ne wanda aiki yake yawo da shi ko ina a Nigeria. A haka ne ya zo Kano inda ya yi gida ya tare da iyalansa. Da yake makotaka suke da gidansu Haidar to sai shakuwa da aminci suka shiga tsakaninsu. Kasancewar Alhaji Sa'adu ba shi da wani dan uwa a garin kano to da ya samu Abbansu Haidar sai ya rike shi ya zama dan uwanshi na kut da kut. Faruk da Haidar sa'o'in juna ne tare suka ta so iyayensu suka sa su primary tare, secondary ma tare Faruk da Haidar sun shaku da junansu. Abun ya wuce abotaka ya koma 'yan uwantaka. Bayan gama secondary dinsu ne aiki ya kuma mayar da Alhaji sa'adu gida wato katsina ya tatara iyalinsa suka koma can gida. Hakan kuwa bai yi wa su Haidar dadi ba sai dai don basu da yanda za su yi ne, to daga nan ne Haidar da yaya Abba suka tafi America karatu. Bayan dawowarsu ne da za a bikin bude masa kamfaninsa da mahaifinsa ya bude masa to sai ya tafi garin mashi ya lalubo Faruk. Bayan bude kamfanin nasa ne dai suka ci gaba da zumuncinsu. To faruk din yayi aure yana zaune kusa da iyayensa Yau Haidar bai samu zuwa office ba don Abuja yake shirin tafiya, don haka tun tara na safe ya kammala duk shirye shiryensa ya nufi hanyar Abuja. A hanya ya lodar musu tsaraba. Bai samu matsala dangane da kwantaccen da ta yi masa, tun da ya san unguwar da suke zaune fitacciyar unguwa ce ta manyan kasa masu fada a ji ne. Kausar kuwa a na can an gama duk wani shirye shirye na taryar gwarzon masoyi. An gyara falo an kayatar dashi, ana jiran masoyi. Kausar ta yi wanka ta sha kwalliya da dandatsetsen less. wanda za mu iya cewa kwalliyarta ce, ta fito mata da kyau. Don kun san ba a mummunar mace sai marar gyara. don duk munin mace kwalliya sai an ga kyata. Don naka gyara da kwalliya shine mace. Kausar baka ce amma a yanzu da yake durfafi yin shafe shafe da mayuka 'yan kanti za mu iya cewa ta koma fara. Doguwa ce, tana da kiba da fati. ba ta da wani girman nono, kanana ne wanda har sun riga sun zube, amma wayayyiya ce ba ta shiga abin da be shafe ta ba akwai hutu da jin dadi rayuwar duniya. Haidar ya iso lafiya. "Ya kuke murna da rawar jiki a wajen Kausar. Tuni ta sa a ka shigar da Haidar dakin da aka wuni ana gyarashi don zuwasa. Tuni aka gama cika gabasa da kololin abubuwan ci da na sha. Can Kausar ta shigo cikin washe baki tana fara'a don bakin yaki rufuwa ta ta ho ta saurin ta ta zauna kusa da shi a guje ta rirrike hannuwansa, "Oh ni 'yar nan! Allah na gode maka da ka sake hada ni da abun sona, burin zuciyata wato Haidar, ubangiji yanda ka hada mu a nan yanzu ubangiji Allah ka hada mu a gidansa a dakinsa, a matsayin matar aurensa,. Ta shafa. Haidar ya ce, "Irin wannan doguwar addu'a haka to kada ki yi wacce za ki rike ni a gidanku na kasa komawa gida. Ta kyalkyale da dariya ta rinka zuba masa girke girgen da aka yi masa kamar ta ba shi a baki haka ta rinka yi masa. Suna dade suna hira duk wani dan gidasu sai da ya zo suka gaisa. Haka ya shiga ciki ya gaida Babarta da kishiyar babarta. Ta hau da shi falon sama har wajen babanta sai da ya ce, Baban nata yayi murna da ganin shi don ya yaba da hankain haidar a kan zai turo iyayensa don a yi maganar aurensu da Kausar. Babanta ya yi ta sa masa albarka inda Haidar din yake ta malala masa godiya. Haidar sun sauko daga saman sun dawo wajen hirarsu Kausar sai munrna take kamar ta goya shi. Ya sa yaron gidansu ya kawo musu tsaraba a but din motarsa ya yi wa kausar sallama don yana so ya tafi gida kada dare ya yi masa a hanya. Da kyar ta kyale shi ya tafi don gani take yi kamar in ya tafi ba zai dawo ba. Haidar daga Abuja duk dumbin gajiyar da ya kwaso bai wuce gidansa don hutawa ba sai ya zarce gidansu, yanda ya shiga a hargitsensa Abba da Aunty suka san ba lafiya ba. Bayan sun gaisa ne ya koma gefe daya ya yi zugum da shi yana tunanin ta ina zai fara ne. Abba ya shi, "Haidar lafiya? Me yake faruwa ne? "Wallahi Abba abun da yake damuna ne na rasa ta inda zan bullo masa bare na gaya muku "Ba komai gaya mana ko meye, kana da wadanda za ka gayawa ne wandada suka fi mu? Ai ka ga babu ko? Gaya mana menene damuwarka?" "Wato Abba tun muna America akwai yarinyar da muka yi alkawarin aure da ita, to bayan mun gama na taho gida Abba kuka tayar min da maganar auren jawahir. Abba don kada na bata muku rai ne shi yasa ban yi muku maganar kausar din ba. Ita dai na gaya mata, na ba ta hakuri, to ta tashi hankalinta sosai, to shi ne na kwantar mata da hankalinta da cewar zan aure ta bayan shekara daya. da kyar Babanta ya amince mata shi ne yanxu kuma uban nata ya takura mata da maganar auren, nake so don Allah Abba ku bar ni na aure ta. Aunty kuwa ta mike tsaye cikin fada take nuna shi da yatsa, "Kai ka kiyaye ni, wallahi ka shiga hankalinka. A aura maka 'yar uwar tawa auren naku shekara daya ka ce za ka yi mata kishiya, to ba ka isa ba ka yi kadan jawahir ta fi karfin ka wulakanta ta." Abba ya daga mata hannu ya ce, "Aisha ya isa haka. Haidar tashi ka je gida tukunna sai mun yi shawara za ka ji komai. Ya mike, "To Abba na gode ku tashi lafiya. Aunty sai da safe ya wuce sukuku kamar wanda kwai ya fashewa a ciki Abbansa ya ce, ba a yin haka Aisha ki duba ki gani yaron nan ya yi mana biyayya lokacin da muka tursasa shi auren jawahir yanzu bai kamata ya zo da tasa bukatar mu ki biya masa ita ba, kin san 'ya 'ya amana ne a hannunmu duk da cewar mu muka haife su to idan muka zalince su Allah fa ba zai kyale mu ba sai ya tambaye mu, to kin ga dai bai kamata da farko mun bi son rainmu mun yi masa aure ya hakura sun zauna sannan yanzu ya kawo bukatarsa mu bi son zuciya mu hana shi, aikin ga ba mu dai dai ba bare lamarin aure da ba ayi masa katsalandan. Abun duniya duk ya dagulewa haidar duk dai da ya ga alamun nasara a wajen Abbansa, to Aunty fa Ai ita za ta zamo babbar matsala. Yana zaune a falon kasa jawahir ita ma tana waje daya zaune kan kujera tana yi wa Sayyid karatun Alkur'ani yana biyawa. Wayar Haidar ta fara ruri ya daga, "Hello Kausar ina gajiya. Ba gajiya sweety, yaya ka dawo gida? "Lafiya lau kausar ai na sha wahalar tafiya dag kano zuwa Abuja a mota kuma a dawo a ranar, ai akwai wahala. Ko da yake ba komai tun da Hausawa sun ce garin masoyi ba ya nisa, duk ranar da Allah ya mallaka min ke na fanshe wahalata...... Wani katutun bakin ciki ne ya tsayawa jawahir a zuciya, rainin hankali wato a gabana ma yake yi wa mace waya? wallahi bai isa ya yi min wulakanci ba, ina zaman dole a gidansa 'yar sakin fuska ba yayi min bare mu yi hira amma shi ne yake kyalkyala dariya da budurwarsa, kawai sai ta mike a fusace ya riga ya shagala da yin magana a wayar ta fizge wayar daga hannunsa ta doka ta da kasa. Wayar ta tarwatse sai ta ya daki a guje ta rufe kofa duk da haka sai ta fada gado ta sa kuka. (To in banda abun jawahir kukan me kike) Bari dai mu ci gaba labari mu ji me yake faruwa a zukatan guda biyun. Haidar ya bi wayarsa da take tarwatse kan kafet da kallo, "To me jawahir take nufi da za ta fizge masa waya? Kishi take yi ko kuma dai ta fara raina shi ne? Lallai zai yi wa tufkar hanci kada nan gaba abin ya shafi aurensa. Da safe ya gama shirinsa ya sauko ya nufi tebir don yin break ya ga wayam babu break bare alamarsa. Ya kwallawa sayyid kira ya fito da gudunsa, "Ina Antinka?" "Tana daki." "To je ka ka kirawo min ita." Ya kirawo ta ta fito yayin da ta durkusa, "Ga ni." Ke me ya hana ki yin break? Kina nufin haka zan tafi office da yunwa.? Kanta yana sunkuye a kasa ta ce, "Ai ca nake za ka biya ta wajen masoyiyar taka ka ci a can. Ke ba na son shirme kin ji ko, tashi ki je ki hada mana break. Bakin ciki ya ishe ta ba abin ta ce ba za ta yi ba ta sabawa ubangijinta. kawai sai ta mike tana kuka ta nufi kicin din. Sai tausayinta ya kama shi yarinyar tana burge shi ko don biyayyarta. Ta gama soya dankali da kwai ta dafa ruwan shayi sai dammaman kunun gyada da ta yi masa kofi daya kamar yanda yake sha lokaci lokaci. Za ta wuce daki ya yi kirata, "Ke zo nan. Ta dawo ta durkusa. Ya ce, "Ta so ki yi break. Ta girgiza kai na koshi. Ya daka mata tsawa. "Ta so mana jinkinta na rawa ta mike ya hada mata ruwan tea me kauri ya mika mata. Ya tura mata dankali da kwai da biredi gaba ya ce, "Ki ci da yawa ko yanzun nan ranki ya baci. Haka ta rinka ci ana hawaye yana kallonta sayyid kuwa ya tafi wajen Dela za ta yi masa wanka. Haidar ya gama break dinsa ya mike ya nufi office jawahir ta kifa kanta a kan tebir din ta ci kukanta ta koshi ta gama ta shafe hawayenta ta koma daki. Sayyid ya shigo an yi masa wanka ta shirya shi ya rinka jijjiga ta dole ta fito ta hada masa break ta koma daki. Zuciyarta tukuku take yi mata sam ta kasa samun sukuni a zuciyarta tun daga wayar nan da ta ji haidar ya yi, "Wato ma ina ruwanta ne da wayarsa.? To me yake neman faruwa da ita ne? ke wallahi na gaji da zaman banza a gidansa ya zo mu yi duk wace za a yi, na cire tsoronsa da shayin komai don ni mutum ce ba dabba ba yanda yake da a gidansu haka nima nake a gidanmu. Yau ma dai haidar daga office da ya tashi gidansu ya kuma waccewa a kan maganarsa ta jiya. Abbansa ya ce, Ka kara hakuri Haidar a bi komai a hankai ba a son gaggawa don gaggawa tana daga shaidan. Aunty ta ce, Alhaji ka rabu da yaron nan, nema yake ya tozarta mu ya bata mana zumunci to wallahi ba ka isa ka shiga tsakanina da dan uwana ba. Abba ya ce, "Haidar tashi ka je gida zan je na nemi Daddyn jawahir din na yi masa bayanin komai, na san shi mutum ne me fahimta ba zai kawo komai ba to daga nan sai mun shirya ranar da za mu je Abujan wajen iyayen yarinyar. Haidar ya rissina, "To Abba na gode Allah ya saka da alheri, ubangiji ya kara girma. Ba komai haidar kai dai ka rike amana kuma ka sawa zuciyarka adalci ya yi musu sallama ya tafi. Yau a falo ya samu jawahir tana kallon wasan Hausa. Be kalli inda take ba ya haye samansa. Ita kuwa daman a cike take ta shi jira take yi ya dawo su yi wace za su yi don ta gaji da zaman gadin gidansa. Sai da ta bari ya kammala dun wani abu dayake yi ya dawo falon kasan ya zauna yana duba jarida sannan ta fara magana ba tare da ta kalle shi ba. "Yaya yau dai magana nake son mu yi da kai. Ba tare da ya dago kai ba ko ya bar karatun jaridar ya ce, Uhm ina sauraronki. Ta ce, "Wai menene matsayina a gidan nan ne? "Bai dago kai ya kalle ta ba ya ce, "Matsayinki kike son sani? Ta ce, "Kwarai kuwa." "Ya ce, "In dai ba mantawa kika yu ba matsayinki yana na kanwata da kuma wai matata ta aure, don wai zance. Ta ce, "To in haka ne me zai hana ka sake ni ko ma huta daga ni har kai da wannan daurin da bai bayin da aka yi mana. Ya ce, mata, "Ai dama ba ni na gayyato ki ba in wanda ya kawo ki ya gaji da zaman naki za ki ga ya zo ya dauke ki. Zumbur ta mike tsaye ta rike kugu ta nuna shi da dan yatsa, "Kai bari ka ji, ni ba irin ballagazayen matan nan ne da ka saba wulakantawa ba, ni na fi karfin wulakancinka, ina bin ka ne gudun kada na sabawa ubangijina da kuma gudun wargajewar zumuncin iyayenmu da nake yi wa biyayya, to yanzu na gaji da zama da kai don ka san ba na son ka a ka ba ni kai, na yi hakurin zaman shekara a gidanka, to yau hakurina ya kare ba zan sake kwana a gidanka ba dole ne ka sake ni. Tana rike da kugu tana yamutsa fuska tare da girgiza jikinta na jin bala'i. Ya kalle ta daga sama har kasa, dariya ce ta kwace masa ya dai daure ya gintse dariyar ya ce, "Ni nan da kika ganni ba zan taba sakinki ba, in kin ga dama ki zauna in baki ga dama ba ki je duk inda za ki amma maganar rabuwa babu don ni ba wawa ba ne. Idan ba ki sani ba ma ki sani aure zan yi kwana nan. Ta dafe kirji, "Aure! Aure fa ka ce? Da gaske kake yi? Wallahi ba zan zauna a gidanka ba bare matar ta zo ita ma ta raina ni, ban da kaddara ma me zai sa na aure ka? Ni me santalelen saurayi da yanzu ina gidansa. Ya mike kuwa cikin sauri zai kai mata mari ta yi saurin kaucewa ya ce, "Ki yi a hankali duk san da kika sake fadar wani namiji a gabana da sunan yana sonki sai kin raina kanki. "Ya yi hayewarsa sama ya bar ta tana kuka. Haka kawai be yi min abun da na nema ba sannan ya ce aure zai yi, wallahi ba zan zauna ba tafiyata zan yi, duk abin da ma zai faru ya faru. "Da sauri ta fada dakinta ta kama hada kayanta tana zuvawa cikin akwati ta turo akwatin da kyar ta kirawo Dela ta ce ta bawa yaron gida ya sawa Haidar a but din motarsa. Cikin rawar jiki ta karbi aiken uban dakinta duk abin da ta san za ta bukata ta sa an kai but. Ta fito da shirinta za ta fita lokacin Sayyid ya tashi daga bacci ya ce, "Aunty ina zaki? Ni ma zan biki. "Ta shafa kansa, "Ka yi hakuri Kayyid zan siyo maka jirgin sama me tashi. Ya makale kafada alamar bai yarda ba. Ta ce, "To je ka dakin Yaya ka ce ya zo mu tafi. Ya ce, "To Ya hau san a guje. Ita ma saurin ta yi ta fice ta shiga motar Haidar ta tashe ta ta tafi ba ta taba tuka mota da kanta ba sai yau, amma ta iya don duk sanda za su fita da direba sai ya koya mata. Haidar yana jin tashin mota ya turo Sayyid daga jikinsa ya mike zumbur sai sannan ya tuna ya bar mukullin motarsa a falon kasa. Ya gangaro falon kasan da sauri yana salati, "Inna lillahi wa inna ilaihir raji un. Hankalinsa ya yi mugun tashi. "Na shiga uku. Kadda yarinyar nan ta yi wani wajen yanzu idan wani abu ya samu yarinyar nan yaya zan yi da rayuwata? Ga Sayyid ya ishe shi da ihun kuka yana kiran "Aunty Dole Haidar ya dauki wani mukullin motar ya saba Sayyid a kafada suka fita. Ya shiga mota a hankali yake tuki yana kallon hanya ko zai hango motarsa da jawahir a ciki. Jawahir kuwa cikin nutsuwa da tsoron ta gudanar da tukinta har ta zo kofar gidan Inna tayi hon megadi ya bude mata ta shiga ta yi parking ta sa shi ya jidi kayanta da yake but ya shigar mata da su cikin falon Inna. Inna ta ce, Lafiya na ganki da kaya? Ta ce, "To lafiyar kenan. Inna ta ce, "Me yake faruwa ne na gan ki da kaya kuma kin rame a kan san da kuka zo, ko ba ki da lafiya ne? Ta ce, "To ba dole na rame ba an aurawa wanda ba ya so na ni yana ta gasa ni ga shi nan ai yau ya koro ni gidanmu ko.?" Inna ta dafe kirji ta ce, "Shi da kansa ya ce ki taho gidan? "Shi ne mana Inna kullum sai dai ya kira ni da tatsitsiya ko kwaila, ya mai da ni 'yar aiki na girka masa ya ci ya koshi wallahi sai kwanan nan ya fara yi min magana amma da ko meye sai dai ya rubuto min a takarda sai ni ma na ba shi amsa a rubuce sai ka ce kurame. Inna ta saka salati, "Au ni ina ta murna na zata ciki ne da ke ashe ba wani bayani. Ta ce, "Uhm inna ke nan, to ko matsayin kyakkyawan kallo ba na samu a wajensa duk na yi hakuri na jure to wai yanzu aure zai yi. Inna ta ce, "Aure, lallai ma yaron nan ban ni da shi boye ki zan yi, zan gyara ki na kula da ke har sai kin zama cikalkiyar mace zai raina kansa ne da ni yake zancen. Duk waigen da Haidar yake yi bai hango jawahir ba har ya iso gidansu. Aunty ya samu a falo tana kallon labarun kasa ya sauke Sayyid ya tafi da gudu ya fada jikin Aunty yana kuka. Aunty ta rungume shi tana cewa, "Haba Auta me aka yi maka kake kuka.? "Bayan Auntyn gidan Yaya ce ta gudu ta bar ni. "To yi hakuri tun da an kawo ka wajena ka ji." Ya daga kai Ta kalli Haidar, "Ina jawahir din take?" Ya ce, "Wallahi ban san inda ta tafi ba, kawai na ji karar mota, ashe ita ta fice ta yi tafiyarta. Aunty ta dafe kirji, "Ita kadai ta ja motar ta fita? Wato ka yi mata maganar auren naka ko? To wallahi tashi ka fita duk inda take sai ka je ka nemo ta. Abbansa ya shigo, "Lafiya na gan ku haka? Aunty ta ce, "To ba dole ka ganmu haka ba, ya salwantar min da 'ya. "Wa ce 'ya?" Jawahir mana, wai be san inda take ba. Abba ya yi saurin zama don jin faduwar gaba da ya yi, ya kalli dan nasa, "Haidar me ya hada ku har ta fita?" Haidar ya ce, "Ni kaina ban san abun da na yi mata ba, ta ji dai ina waya ta kwace wayar ta tarwatsa ta sai na mike na hau sama, to ban ankara ba na ji tashin motata. Aunty ta ce, "Uhm ka ji ba, in ban da rainin hankali yaushe zai je gabanta yana waya da budurwa suna hirar aure. Ni na san wannan rawar kan da kake yi sai ka jawo mana tashin hankali, ka ga in ka ga ba hali ka sakar min 'ya mu ba neman kai muke yi da ita ba. Abba ya ce, "Duk haka ba ta taso ba, ku kwantar da hankalinku da safe zan je gidan na su sai na ji dalilin tahowar tata. Yanzu tashi ka tafi gida. Aunty ta ce, "Ba fa tabbas din gidan ta tafi dole ne a yi binkicen ta tun daga yau." Ta dauko mayafinta ni bari na je gidan na su yanzu. Ta shiga mota direba ya ja ta suka nufi gidansu jawahir. Tana shiga gidan ta tarar da mommy da Nasir da su Auwal da Sani. Aunty ta zauna duka suka gaishe ta cikin fara'a ta amsa tana wasa da dariya ta su. Suka gaisa da momy da tsokana irin wasan nan na kannan miji. Ta ce, "Yaya kuwa yana nan? Momy ta ce, "Eh yana sama. Auwal je ka gaya masa Aunty ta zo, "Ya hau da saurinsa ya sauko ya ce, "Ki hau saman Ta hau. Bayan 'Yan gaishe gaishe da suka yi sai ta gyara zama ta ce, Yaya ina Jawahir din?" Cikin mamaki ya ce, "Au ta zo ne? "Uhm wai rigima suka yi da mijin nata ta taho. Ya ce, "Ikon Allah ai ni ban ma sani ba bari na tambaye ta Ya dau waya ya kirawo momy ta yi sallama ta shigo ta nemi waje ta zauna. Ya kalle ta ya ce, "Ina jawahir take? Momy ta ce, "Tun da aka yi auren ta ba ta zo gidan nan ba. Wani abu ne? "Wai sun yi rigima da mijin ta taho. Momy ta ce, "Oh ni 'yasu, yara ne ka haife su ba ka haifi halinsu ba, yanzu duk fadan nan da aka yi wa jawahir sai da ta sabawa nijinta. Aunty ta ce, "A'a ai ba laifinta ba ne, da ai lafiya suke zaune auren nan da ya rakitowa kansa duk shi ya hargitsa musu zaman." Momy ta ce kin ji irin shashancin ko, ai komai na Allah ne, namiji da aka halicce shi don mata hudu ka hana shi kara daya. Aunty ta ce, A'a ba ta fa da laifi ko ke da kika girma da Yaya ai ce zai kara aure da sai kin hana mu sakewa bare ita da ga yin aure shekara daya a ce namiji zai maka kishiya, ai dole a ji kanku. Dady ya ce, Ai kun san ma ba za ta zo nan ba tun da ta san ba goyon baya za ta samu ba. Tana gidan Inna, tun da ta je hannun Inna kuwa kwato ta sai wani ikon Allah. Aunty ta ce, "Ai maganinsa kenan wallahi gwanda ta hora shi tukunna. Momy ta ce, "A'a ni dai ba na son son kai don dai kin ga 'yarki ce kawai kuke son ga sa masa gyada a hannu. Dady ya ce, Ba me wahalar min da da, duk zan tara su na san meye matsalarsu. Hankalin Haidar ya kara mummunan tashi yayin da ta bayyana cewa jawahir ba ta gidansu. Goma na dare Haidar ya isa gidan Inna a gigice yana neman jawahir din. Inna ta fututtuke ta ce ita yaushe rabon da ta ga jawahir ma? Wallahi ya je duk inda jikarta ta take ya nemo mata ita in ba haka ba kuwa ya gamu da fushinta. Haidar kamar zai yi kuka magiya yake yi wa Inna idan ita ta boye jawahir ta fito da ita don ya ga motarsa a gare jin gidanta wadda da ita jawahir din ta fito. Inna ta ce, To sai dai in zuwa ta yi ta ajiye motar ba ta shigo ba ta fice, "Ta ce, "Na gaya maka wannan kame-kamen ba zai yi maka ba, ka je ka nemo min jikata. Sha daya na dare ya bar gidan Inna ya isa gidansa. Ikon Allah ne kawai ya kai shi gida, amma haka ya kwana yana juyi da tunanin inda za a ga jawahir. Ga yunwa ta gallabe shi ga ba abinci, shi kuwa ko ruwan shayi be iya dafawa ba, bare ya dafa ya sha. Haka ya yi ta juyinsa har aka yi, sallar asuba. Daga masallacin gidansu ya taho a motarsa. Abba ya yi mamakin ganinsa inda yake tambayarsa, "Lafiya haka da asuba.? "To Abba ina zan iya samun sukuni ba a fa ganta ba. "Ba ka ce ka ga motar gidan Inna ba.?" "Ai Inna ta ce ita ba ta shigo mata ba ajiye motar ta yi ta san tana waje. Allah ya kyauta, Abba ya lallaba shi ya yi wanka suka yi break tare. Abban ya dauko shi suka yo gidan Inna wai ko za su ga jawahir din. Amma Inna tana jin tsayuwar mota ta tura ta wani dan daki ta yi zamanta a falo. Abba da Haidar suka shigo duk yanda suka yi don su bigi cikin Inna su ji ko jawahir tana gidan Inna ta fututtuke ta ce ba ta zo mata ba. Dole suka hakura suka yi mata sallama suka fita. A mota kawai Haidar sai ya sawa Abbansa kuka, "Don Allah Abba ka tainaka min a ga jawahir, yanzu in ban gan ta ba ai na shiga uku ya zan yi da rayuwata? Ya dafa kansa ya ce, Ka yi hakuri Haidar za a ganta ne insha Allahu. Bayan fitarsu Inna ta yiwa danta Aminu da yake Abuja waya ta gaya masa komai ta ce tana so ta turo masa jawahir nan kada ya sake ya ce tana gunsa. Aminu ya amsa da to! Ya ce da kansa zai zo tararta filin jirgi. Jawahir ta gama shirinta a boye direban Inna ya kai ta filin jirgi ta hau zuwa Abuja sai da ya ga tashinsu sannan ya dawo ya shaidawa Inna. Can kuwa Uncle dinta yana Airport yana zaman jiranta. Yana hango ta ya taro ta da murna suka rankaya zuwa gidansa matarsa Maryam ta yi farin ciki da ganin jawahir, don Maryam mace ce mai faran-faran da son jama'a ga ta wayayyiya. Irin gogaggun matan nan ne wadanda suka san makamar kama da namiji. Ba bata lokaci Uncle ya karbi takardun makarantar jawahir ya samar mata University of Abuja. Ba bata lokaci jawahir ta zamo daliba a jami'ar. Jawahir an shiga cikin wayayyun 'yan matan jami'a ta goge ta kile, ta kara kyau da girma babu yanda za a yi wanda bai yi mata cikakken sani ba, ya gane ta, don yanda Maryam ta ke gyara ta kamar 'yar cikinta don wani magunguna da tsumi na mata da take dibga mata tana sha. Sai maganin ciko da nono da tsaitsayar da su don har ya zube, shi take ba ta tana sha. Kasancewar hankalinta a kwance yake ta yi 'yar kiba ta murje jikinta mulmul kamar na jariri, sabon haihuwa. Kirjinta ya cika fam yana tsaitsaye ba shi da alamar rankwafawa, duk wanda ya kalle ta sai ya juya ya kara kallonta saboda tsabagen haduwa da wani shirtaccen kyau da ya kara bayayyanar mata. (((((((SALON SO))))))) ((((PART 19 TO 20)))) : BY SULAIMAN MUSA MUHAMMAD (BOMBOY). . HAIDAR ya kasa samun nutsuwa dole ya nufi gidan abokinsa Faruk don yanke shawarar da za ta fisheshisu. Yana zaune a falo Faruk ya hada kai da guiwa yana ta tunani tare da karanta wasikar jaki. Faruk ya shigo falon tare da yin sallama. Bai jira an amsa sallamar ba don ya san ba zai samu ba ya karaso ya dafa kafadar Haidar ya ce, Me yake faruwa ne da kai aminina? Wace matsala ce kuma take kokarin danno maka kai ne? Kai da za ka yi auren ke ce raini. Ya ce, "Kyale ni Faruk abin duniya duk ya dame ni, ko ka san jawahir ta gudu ban san inda ta nufa ba. Faruk ya dafe kirji ta gudu fa ka ce? Me ya hada ku, ko na ce me ka yi mata? "Uhm kai dai a yi sha'ani, wai daga na yi maganar aure zan yi sai yarinya ta gudu. Faruk ya ce, "Ai madallah ka ga irin abin da nake jiye maka ko, to ai ga irin ta nan yanxu sai ka je ka bunciko ta a duk inda take. Haidar ya ce, "Wallahi ni dai ina zaton tana gidan Inna don mota ta da ta dauko ta taho da ita, na ganta a gidan Innan. Sai dai amma Innan ta kafe ta ce jawahir din ba ta gidanta. Faruk ya ce, Ka ga taso mu kaje kawai mu shammace ta ba tare da munyi sallama ba mu shiga kawai in tana ciki za mu gan ta. Suka mike suka yi gidan Inna Haka suka danna kai falon Inna babu sallam abun mamaki ba jawahir sai Inna da ta yi zumbur za ta tashi ta ce ni har kun tsorata ni lafiya kuka shigo min haka babu sallama? Faruk ya durkusa yana gaishe ta Haidar kuwa zubewa ya yi a kasa yana yi wa Inna magiya inna don Allah don Annabi Inna ki taimaka ki fito min da jawahir. Inna ta ce, Haidar me kake fada ne? Ni na san inda jawahir take ne? Faruk ya ce, "To ai ni abin da ya fi ba ni mamaki ya a ka yi motar ta zo nan gidan, "Inna ta ce, "Ni dai ina zaune aka aiko min da mukullin motar na ajiye na zata ma ko tare suke da Haidar din motar ta lalace musu suka ajiye ta, su je su dawo. Ta mike ta shiga dakinta ta fito ta ce ga mukullin motarka nan kada ku sake zuwar min idan ba jikata kuka gano min ba. Haidar cikin marairaita kamar zai yi kuka ya ce, "To yanzu Inna ya za a yi da neman jawahir din.? Cikin fada ta ce, To ya za a yi kuwa? Da ka rike ta hannu bibbiyu ai da haka ba ta faru ba ko? Yanxu da ka yi sakaci da ita ta bata ai ko wa sai ya huta. A dauki yarinyar nan cikin girma da mutunci 'yar uwarka ta jini a baka amma ka rinka wulakanta ta. Ya yi saurin cewa, "Wallahi Inna ba wulakantata nake ba wai don kawai na ce, zan kara aure shi ne ta yi tafiyarta. Inna ta ce, "Uhm ai ka ga yanzu ta bar maka filin gidanka ka fi sakewa kai da Amaryar taka sai ka je kai ta yo auren. Faruk ya ce, "Inna hakuri za a yi in dai an san inda take din a fada mana. Ta ce, "To ban sani ba ku tashi ku ba ni waje. **** ****** ****** Maganar jawahir kuwa tana gidan Ankul dinta ta dage da karatu don makaranta biyu zan ce take yi. Tana zuwa jami'a yayin da kuma Ankul dinta ya daukar mata lakcara guda yake dada tunasar da ita da nusar da ita halayyar dan Adam, yanda ake iya zama da su sannan yana koya mata dabaru na iya kasuwanci da yanda za ka sarrafa kudi duk kankantarsu don juya su. Ta bangaren jawahir kam ma iya cewa Alhamdullihi, don komai a ka gaya mata ya zauna a kwalkwalwarta kenan da yake yarinya ce me kaifin basira da kokari. Jawahir ta gama nazarin abun da aka yi musu lakca a yau ta mike a gajiye ta shiga toilet ta yi wanka ta gama shirinta ta fito falo ta samu Auntynta a zaune. Maryam ta kalle ta tayi murmushi, "Tubar kallah 'yar gidan Ankul ba dai kyau ba, zo ki zauna na dora miki inda muka tsaya don so nake yi ki mallake Haidar tsab yanda ya raina ki yake kiranki da tatsitsiya ko kwaila to yanzu ki zame masa dan hakin da ka raina. Yanzu abin da zan fara miki da shi shine zan koya miki kissoshi kala-kala don haka dauko littafi da biro ki rubuta komai don gudun mantawa. (Saboda haka idan kuna so nima na fada muku to kowa ya/ ta dauko biron shi/ta domin nima saida na rubuta sannan na iya kawo muku badon haka ba........hmmm. Gani nan ina zagayawa fa. Hhhhh su o'o akwai akwai tsoro ji harda rawar jiki kar na ganta ba paper). Jawahir ta mike ta dawo da littafi da biro, "To yanzu za mu fara da kissar tsafta don ita ce kan gaba a kan komai. Ki kasance mai tsaftar gidanki ko da yaushe cikinsa da wajensa. Kicin dinki ya zamo a gyare a share, a goge ki turara masa turarukan wuta me dadin kamshi. Toilet dinki ya zamo kullum cikin gyara idan kika wanke kika goge komau kika cire yana ki masa nasa turaren wutar na musamman ya kasance cikin kamshi wanda mutum ya yi bahaya wannan kamshin zai kashe masa jin warin bahayan nasa, idan ba ki da lokacin yin wanki da kanki to a ajiye almajiri idan sun kai kala biyu zuwa uku ki ba shi ya wanke ya goge miki, idan kin tashi sai ki turare kayan naki da turaren kaya sannan ki jera a kwaba. Sai kuma kwabar ki sa mata turaren kaya don gudun warin ruma da dai sauransu. Ki kasance mai kwasar shimin mijinki, gajeren wandonsa, hankijinsa da dai wani karamin abu da yake amfani da shi ki wanke, ki goge su ki turare su da turaren kaya ki adana masa su. Idan kin shiga wanka ki rinka amfani da daddadan sabulu me kyau da dadin kamshi. Ki rinka cuda hammatarki, kasan nonuwanki, matse-matsin cinyarki, ki rinka wanke gabanki sosai da sabulu me kamshi, duk wani lungu da sako na jikinki ki wanke shi ki gyare shi fes in da ko ina mai gida ya sa kansa zai ji kamshi. Ki kasance ko yaushe cikin gamsasshiyar kwalliya, ki daure da asuba idan kun yi sallah me gidanki zai ja ki ku koma gado ku kwanta, to ki yi kokarin hana kanki bacci. Har sai shi ya yi sai ki janye jikinki a hankali ki tashi ki nufi kicin don hada muku karin kumallo. Kada ki yi masa break kala daya saboda saurin ginsa ki yi masa kalolin break kowanne ki zuba a fulas gudun kada ya huce. Daga nan ki jere su a tebir ki gyara wajan ki da turare ko ina da daddadan kamshi me sanyaya zuciya, sai ki je ki yi wanka ki bata lokaci wajen yin kwalliya wannan fa kwalliyar safe ce ta barka da tashi me gida. Za ki saka les ko atamfa ko shadda ko boyal duk dai wanda ya samu, za ki feshe jikinki da kalolin turaruka masu kyau da dadin kamshi wanda har za a kasa tantance wane irin kamshi kike yi, to sai ki nufi dakin maigida. Ba a tashin miji da hayaniya ko surutu ko ki yi ta jijjiga shi kina kiran wane! ka tashi lokaci ya yi, in kika yi irin haka za ki bata ran maigidanki. Abin da kawai za ki yi shine da kin shiga dakin mijinki kin ga yana bacci ga lokacin tafiya Office ko kasuwa ya kusa, to sai ki zauna a gefen gadon ki sa hannuwanki kina shafar fuskarsa kisa bakinki kina hura kunnunsa a hankali kina shafa fuskarsa tare da dan jan karan hancinsa. Ko ki fara shafar kasan mararsa kadan-kadan. To za ki ga ya tashi a nitse ba tare da magagi ko tsaki ba, da ya mike ya shiga toilet ko kafin ya fito sai ki yi saurin gyara gadon ki debo masa kayan da zai sa hade da best da gajeran wando da dan hankici duk kuma ki feshe su da turaruka masu dadin kamshi ki debomasa takalmansa ki goge su fes, da ya fito daga toilet ki yi gaggawar daukan tawul ki rinka tsane masa ruwan jikinsa sannan ki debo mayukan da yake amfani dasu ki rinka shafa masa a hankali kina yi kina ba shi labari na ban dariya a hirar nishadi. Ki taimaka masa wajen sa kayan nasa, ki sa karamin kum ki taje masa sumar kansa, ki dada dauko turaruka ki kuma feshe shi da su, ki sa masa gilas idan yana da ra'ayi. Ki riko hannunsa ku taho zuwa kan tebir kuna tafe a hankali kina yi masa rausaya tare da yawan shigewa jikinsa har ku iso tebir din. Ki rinka zuba masa komai kina turo masa gabansa kada ki damu da sai kin ci a lokacin, ki rinka hada masa abinci me yawa a gabansa ki rinka tura masa kina yi masa shagwabar bai ci da yawa ba, ko ki ce ke ba ki yarda ba sai ya cinye da sauran abubuwan da za su ja hankalinsa ya saki jikinsa sosai ya ci abinci ya koshi. Idan ya mike don ya tafi office ki roko masa jakarsa kina yi masa 'yar shagwabar Honey da ka tashi daga office ka yo gida kada ka tsaya wani wajen ka ji. Honey idan ka isa office ka tsaida hankalinka ka yi aikinka a nitse kada ka yi tunanin komai bare ya sa min kai a damuwa. Za ki ga ya rungumoki tare da shi miki albarka duk kuma inda yake hankalinsa yana kanki Allah Allah zai yi ya dawo gida don ya tarar da ke. To da ya tafi office ke kuma a wannan lokacin za ki samu ki yi baccinki kafin lokacin girkin rana ki kula me mijinki ya fi so, me ya fi sha awar ci don ki kiyaye wajen girka masa su, shinkafa da miya, ko tuwon shinkafa da miyar taushe, ko danyar kubewa, ko miyar agushi, ko miyar wake da ganye, ko tuwon dawa, ko na masara, tuwon semovita ko ki daka masa sakwara, ko ki dafa kuskus ko taliya, zaki hada masa da soyayyen naman kaji ko gasasshen naman kasuwa ko farfesun kayan ciki, ko farfesun kan rago ko na jelar sa ko farfesun naman karamar dabba, ( A nan ana magana ne idan mijinki mai hali ne, idan kuwa ba mai hali ba ne sai ki yi masa abin da kika tabbatar yana jin dadinsa dai-dai rufin asiri) To idan kika duba abin da ya fi so a cikin yi masa kika gama komai kafin ya dawo, ki dada gyara gidanki ki turare shi da nau'in kamshi kala kala, ki shiga aiki sake fesa wanka sai ki yi kwalliya ki hade da siket ko riga da wando ko doguwar riga ko dinkakken shadda, ko atamfa, boyal, yadi, material, da dai sauransu, to ya kasance karamin dinki ne dai-dai jikinki ki saka wanda da zarar maigida ya dawo za ki tafi cikin salon murna ki ringume shi kina me yi masa barka da zuwa. Ki fara raka shi dakinsa ki cire masa kayan jikinsa ki hada masa ruwan wanka da turaren wanka a ciki da ya shige tolet sai ki kwashe kayan da ya cire ki rataye masa a anga. Ki fito masa da kanana na shan iska. Da ya gama shirnsa ya fito sai ki zo a nitse cikin dabara ki rinka loda masa abinci yana ci kina fara loda masa wani yanda zai ci ba tare da ya gane ya ci da yawa ba. Kina zuba masa sanyayyen abin sha yana ci yana sha, har sai ya koshi ya yi kat sai ki jawo shi ku baje kan kafet ko kujera kuna wasanni da hirarraki masu dadi ko kallo ku, ki rinka karanta masa labarai masu dadi, amma ki kasance ko yaushe kina manne a jikinsa ki rinka yi masa shagwaba kina mai da kanki karamar yarinya a gabansa kina zama doluwa marar wayo ki rinka sa yin dan sokoncin zai rinka sa mijinki dariya, to yawaita masa irin wannan abubuwan shi zai kara muku shakuwa da fahimtar junanku, za ku kasance cikin bege da son junaku ko da yaushe. Idan kin tabbatar kin wa mijinki lodi da abincin rana to yunwa ba za ta gallabe shi da dare ba, don ba a so da daddare a ci abu me nauyi an fi so a ci irinsu hadin salak, sharfar taliya me romo gasasshen nama, ko hanta ko zaka, farfesun kayan ciki ko na naman romon kai, ko na jelar sa ko naman karamar dabva, kai da dai duk abin da Allah ya hore muku marar nauyi. To kinga wadannan duk inya ci va za su yi masa bauyi a ciki ba bare su hana shi su kuni su takura shi wajen aiwatar sa sunnah Jan hankalinsa ta suffofin kwanciya kala-kala. Duk abin da kika kula ya fi so to ki lakanci abun duk sanda kuke tare ki rinka kirkiro wasu abubuwan ma da bai san da su ba. Ki saki jikinki da shi ki cire kunya ki rinka sarrafa shi kina dan kukan kissa tare da kiran sunansa a hankali kina hadawa da kalaman soyayya don tafiyar da imaninsa. Ki kasance cikin yawan shan kunun aya, shan zuma, shan rake, lemon zaki, kankana, gwanda, abarba, nono, dabino, cukwi, tufa, inibi, kin ga wadannan ki kasance cikin yawaita cin su ko da yaushe don suna karawa mace ni'ima da amfani sosai a jikinta. Ki nemi garin bagaruwa gwangwani daya, garin kurna gwangwani uku, garin habbatus sauda rabin gwangwani, garin dakakken dabino ki rinka samun busasshiyar aya ki daka sai ki hada su waje guda ki samu lafiyayyen nonon shanu marar tsaki kina diban wadannan kayayyakin da kika hada kina damawa da nonon kina sha, to wannan shi ne sirrin yanda kika ga nonuwanka sun cuccuko sun yi manya suna tsaye ba su da alamar rankwafawa. Jawahir ta ce, "Au Aunty kina nufin garin nan da kike ba ni damamme da madarar shanu yana da nasaba da cikuwar nonuwana?" Aunty ta ce, "Kwarai kuwa shi ya sa kika ga ina yawan gasa mana naman karamar dabba ruwa ruwa da kuma romon kai da farfesun wannan sirrika ne na mata. Duk abubuwan da na lissafo a baya su suke bamu ni'ima a jikinmu mu mata suna sa ihu kyan fata, yawan, amfani da man zaitun da habbatus sauda suna sa fata ta yi mul-mul da santsi kamar ta jariri." Jawahir ta ce, "To Aunty ni da ba a gidan miji nake ba amma kike ta dirka min magunguna da tsumi ina sha. Kuma kullum sai kin sa ni na yi turare na tsugunno da na jiki, meye fa'idar hakan.? Ta dafa kafadarta daya ta ce, "Diyata ke nan, ai duk wannan shiri nake yi miki nake tsumaki don duk sanda Haidar ya kusance ki to haihaita haihaita sunyi sallama da kowacce irin mace don ba me iya gamsar da shi sai ke, na gaya miki Haidar sai ya dawo tafin hannunki, sai yanda kika juya shi. Jawahir ta fada cinyarta tana kyalkyala dariya, "Na gode Aunty sai ya san wadda yake cewa kwaila ko tatsitsiya." (((((((SALON SO)))))) (((PART 21 TO 24)))): : BY SULAIMAN BOMBOY: . Bangaren Kausar kuwa kullum cikin yowa Haidar waya take safe, rana, yamma da dare ma ba ta bar shi ya huta ba kan maganar aurensu tun yana boye mata yana cewa ta jira shi har dai ya fito ya gaya mata gaskiyar batun matarsa. Amma ya ba ta hakuri da ta jira iyayensu su dan samu nutsuwa sai ya tada maganar su zo. Amma da ta kai ta kawo yau da Kausar ta tayar da hankalinta sosai don gani take yi kamar Haidar din sake subuce mata zai yi a karo na biyu, ganin yanda ta samu kanta ne ya sa Haidar ya je yake tuntubar mahaifinsa da zancen. Abbansa ya ce, Yanxu Haidar ba za ka hakura da auren nan ba, kana kallon maganar nan ce ta tayar muku da rigima ga shi ba a san inda 'yar uwartaka take ba ko? Haidar ya ce, Abba ka tausaya min mana, yau shekarar jawahir daya kenan da barin gidan nan. Abba kana kallon kullum ina hanyar gidan nan don cin abinci ni ba na iya cin abincin waje bare na rinka zuwa Otal ina ci. Abba ba ka tausaya min na samu na yi auren nan ko ni ma na samu nutsuwa a gidan? Abba ya ce, "Yanxu kana ganin idan ka yi aure surutun mutane 'yan uwa da abokanan arziki ba za su dinga ganin ba ka damu da batan matarka ba? Ka ga abin zai zama abin surutu ko? Haidar ya ce "Wallahi Abba jawahir tana hannun inna don ita ta boye ta. Ya ce, "Ka tabbata? Daga bakin wa ka ji? Wallahi Abba migadin gidan Inna na ritsa na ce ko ya gayan gaskiya ko na debo masa 'yan sanda shi ne yake gaya min tana gidan Inna to idan na je wa da Inna maganar sai ta koro ni, ni dai ina ganin gwara na yi auren in ta ga na yi auren za ta dawo da ita. Abba ya ce, "To shi kenan Allah ya zaba abin da ya fi alheri, zan je wajen Alhaji ibrahim din duk abin da muka tattauna sai ka ji. Ya ce, "To Abba na gode. Ya mike ya tafi. Abban Haidar ya samu Dadyn jawahir yake gaya masa yan da suka yi da Haidar din, Alhaji Ibrahim ya ce, ai ni tun da na ga hankalin Inna bai tashi ba na san cewa jawahir tana hannunta. To na sha tuntubar Aisha a kan maganar, to idan a ka bar maganar ai anyi zalinci kuma an shiga hakkin Haidar, shekara guda mace ta gudu ta bar ka kuma a hana ka yin aure, ai da zalunci, ni dai kawai ina ganin in Allah ya kai mu jibi mu je gidansu yarinyar a gama maganar komai Haidar ya samu mata kawai Lokacin da suka je Abuja gidan kaninsa Alhaji Aminu suka sauka tukunna sai da suka huta suka samu nutsuwa sannan suka dinguma har Alhaji Aminu zuwa gidansu Kausar. Sai bayan tafiyarsu sannan jawahir ta dawo daga makaranta. Antinta take bata labarin zuwansu Dadynta, Jawahir gabanta ya fadi, "Lafiya kuwa Aunty.? "Eh to, wallahi ban sani ba don sun tafi tare da Ankul dinki kuma be gaya min inda za su je ba ko dalilin zuwansu ba. Jawahir ta ce, "To Allah ya sa dai ba ganowa suka yi ina nan ba. Amin da 'yata, don ba na so a raba ni da ke. Suka yi dariya. Gidan su Kausar an yi wa su Alhaji kyakkyawar karba inda iyayenta suka nuna karamci da dattako. A lokacin mahaifinta ya ce ya yanke ranar aure sati biyu masu xuwa kawai nan fa a ka yi ta murna ana sa musu albarka. To su Alhaji su daga nan suka hawo jirgi suka juyo gida shi kuma Ankul din ya koma gida. Suna zaune da matarsa a falon suna tatraunawa jikin maryam duk ya yi sanyi da jin abin da ya kawosu, Alhajin Abuja. Jawahir ta shigo falon tare da yin sallama ta tafi kusa da Ankul dinta ta zauna dab da kafarsa a kan kafet ta ce, "Ankul barka da dawowa. "Yauwa 'yata sannu "Ankul me ya kawo su Dady? Ko sun san ina nan ne? Ya girgiza kai, "Dady bai san kina nan ba kawai abin da ya kawo su ne, shine na yi musu rakiya. Ankul Dady bai tambayeni ba? "Ai bai san kina nan ba ne shiyasa. "Ankul ko dai maganar auren Haidar ce ta tashi suka zo suka gaya maka?" "In ban da abinki idan auren Haidar ne ai sai su yo min waya ba sai sun zo ba ko? "Eh to, haka ne Amkul'" ya ce, "Kwaso littattafanki mu gani, "Ta mike ta nufi dalinta. . ***** ****** ***** Lokacin da suka isa gida suka shaidawa Haidar halin da ake ciki, a satin suka hada hada kayan lefe da komai da komai mata suka kai, duk wannan halin da ake ciki hankalin Haidar yana kan jawahir don haka ya je ya shirgo mata kayan fadar kishiya akwati uku hadaddun kaya na gani na fada, don tsadaddu ne a ciki ya ai ka wa Inna ya ce a gaya mata tun da ta rike masa mata matarsa ta hana shi to ga kayan fadar kishiya ne don ba a gaya musu da baki ba. Inna ta karbi kayan ta samu waje ta adans su. Biki ya zo bangarensu Kausar sun sharyawa bikin don kalolin fatin da za a yi da komai da komai Kausar ce ta bude bakinta ta yi ta hidimarta ba ta jiran ango don ta san halinsa auren ba dada shi ya yi da kasa ba, ta yi hidima da bidirinta. Fati daya kawai Haidar ya je shi ma, sai da ta dame shi da magiya sannan ya daure ya je. Amarya ta tare a gidan angonta Haidar. Babban falon gidansa na amfanin kowa da kowa ne, a falon akwai kofa da take kallon gabas ita ce in an bude an shiga sashen jawahir da katon falo da dakuna uku a ciki, sai toilet, kicin da suke a ciki. To idan an dawo falon akwai wata kofar da take kallon yamma wato tana kallon kofar bangaren jawahir to ita ma in ka shiga katon falo ne da kicin da tolet shi Amarya Kausar ta shiga, to a tsakiyar babban falon bene ne wanda za ka hau ka je turakar megidan, shi ma falon falo ne, da ya kushi dakuna biyu na bacci da tolet da kicin, sai wata kofa da za ka bi a saman dai, shi kuma makeken fili ne da aka kayatar da shi aka yi masa rumfa don hutawa, to nan saman shi ne na megida Haidar. Zama ya yi dadi tsakanin Ango da Amarya sai dai sabanin halayya da ta zo bamban ta ango da amarya, don ita Kausar ta samo masu yi mata aiki har mutum uku ta cika masa gida da mutane ke nan, shi da yake dan hutu ba ya son hayaniya, to amma duk dawowar da zai yi zai tarar da Kausar uwar lalaci a mike a doguwar kujera ko kan kafet masu aikinta suna yi mata tausa, wani karin abin haushi wai ba ta iya girki da kanta sai dai me aiki ta yi musu wannan dalili shi yake hana shi cin abincin gidan, an gudu ba a tsira ba kenan, don kullum sai ya biya ta gidansu ya ci abinci Karin abin da yake bawa Haidar Haushi da Kausar wai gadon da suka kwanta sai dai ta kirawo me aiki ta gyara, wai ina abubuwan da jawahir take sanya musu a gidan da dakunansa suke kamshi ne, duk yanzu wannan kamshin mai dadi babu. Shi wai shi yaya zai yi ne ya dawo da jawahir dinsa ne, ko don lafiyayyen girkin da take yi masa mai dadi ga ladabi da biyayya, duk yanda ya bata mata rai ba za ta fasa yi masa girki ba ko ta ki gaishe shi, ga shi ya yi auren wayayyiya wadda ta yi karatu a waje amma babu biyan bukata. Don zamansa da tatsitsiyarsa ya fi sau dubu dari, duk hanyar da ya bi don Inna ta dawo masa da jawahir ya bi amma magana daya take gaya masa ita ma ba ta san inda take ba. . Lokacin da jawahir ta ji labarin auren Haidar ta yi kuka sosai ta tashi hankalinta har sai da Inna ta zo Abuja don rarrashinta. Don lokacin Ankul dinta yana legos. Jawahir kuka take kamar rainta zai fita Inna kuwa sai sai rarrashinta ta ke yi tana bata hakuri jawahir ta ce, ni ba wani abu ne ya sa ni kuka ba irin yanda ya wulakanta ni ya yi aure kin ga ya sake nunawa duniya cewar bai damu da ni ba kenan. 'Inna ta tausayawa jawahir don ta fuskance ta kishi ne yake damunta. Inna ta ce, "Ki yi hakuri idan kina so ma yau sai na mayar da ke gidanki. "Da sauri jawahir ta dago kai tare da saurin katse Inna, "Haba-"Haba Allah ya sawake ai sai ya ga na damu da shi ne ya sami hanyar da zai kuma wulakanta ni. Inna ta ce, in dai wannan kike ji kwantar da hankalinki domin kuwa yanzu Haidar ta damu dake wanda ba kya zato, auren nan da ya yi ya yi shi ne don na yi fushi na dawo masa da ke ne, ta ba ta labarin yanda hankalin Haidar ya tashi na rashinta da yanda a kayi auren har kayan fadar kishiyar da ya kai mata da irin korar karen da take yi wa Haidar din, ko ba komai in kalaman Inna ya sanyayawa jawahir zuciyarta har ta ji tana sha awar ta koma gidan Haidar ko dan ta ga wanne irin zama suke yi da Amaryar ta sa. Jawahir ta ce, "Shi kenan Inna ba komai Allah ya kara rufa asiri. Kwanan Inna biyu a Abuja ta juyo zuwa gida, Maryam ta ce da jawahir kada ki damu diyata, ni na san shirin dana yi wa jikinki kowanne namiji in dai ya dandana ki to ba ba zai iya kusanta ki da wata mace ba, ni na fada miki haka kuma ki hakura ki koma gidan Haidar ko don ki ba ni labari gaba, idan ya dandani zumarki. Jawahir ta ji kunya ta mike da gudu ta bar wajen. Bayan Inna ta koma gida washegari ta nufi gidan danta Alhaji Ibrahim mahaifin jawahir, su momy da Abba Nasir zuwa su Auwal da Sani sun yi murna da ganin Inna gida ya rude a na ga Inna ga Inna. Inna ta zauna cikin jikokinta ana wasa ana dariya Momy kuwa tana ta hidimar kawo mata ababan ci da na sha. Momy ta zauna suka gaisa Inna ta ce, "Maigidan kuwa yana nan.? Momy ta ce, "Eh yana nan bari na yo miki magana da shi." Momy ta samu Dady rigingine a kan gado yana kallon sili da alamu tunani yake yi, Ta yi sallama tare da cewa, "Barka da hutawa. Ya amsa da yauwa: Inna ce ta zo take son magana da kai. "Ya mike zumbur ya ce, "To gani nan fitowa. Ya zo ya durkusa har kasa ya gaida Inna, ya ce "Inna da kanki kika taho maimakon ki aiko na zo.? Ta ce, "Kamawa ta yi daman na zo a kan maganar yaran nan ne, ya ce, "Wanne yara?" "Ta ce, "Wanda ka hada auren dole yanzu kuma kuka je kuka yi masa auren da yake so, ita kun hana ta wanda take so ta mutu kenan ko.? Ya ce, "Inna Allah ya ba ki hakuri wallahi ba haka ba ne." Dady ya ce, "Don Allah don Annabi Inna ki yi hakuri kada ki yi haka ba mu san abin da auren nan ya kunsa ba, kada mu yi wa Allah shisshigi a lamarinsa. Yanxu ki yi hakuri ki dawo da jawahir nan gidan gobe sai na sa a mayar da ita gidanta. Inna ta katse shi, "Kana nufin a mayar da yarinyar ya ci gaba da wulakanta ta ko? "Wallahi Inna ni na san ba zai wulakantata ba, in kika yi la'akari da yanda ya gigice da batan jawahir din. Inna ai kun hora shi ya horu ba zai sake ba. Inna 'ya 'yan nan duk namu ne wa za mu ki a cikinsu.? Duk wanda za ta aura ai ba kamar Haidar din ba ko Innata? Ta ce, "To shi kenan ai kokarinka ni ma na fi son a karfafa zumunci. "Yauwa Innata yanxu ina jawahir dina? Tana can gidan kawunta. Dady ya rike baki "Wanne kawun nata? "Tana da wani kawunne bayan Auta Aminu?" Alhaji ya ce, "Ikon Allah yanxu duk binkicen nan da muka yi ta yi tana Abuja.? Sallamar Haidar da Abbansa ne suka shigo nan fa Abban ya nufi Innar ya durkusa gaban Inna yake gaishe ta, "Haidar kuwa gaban Dady ya je ya gaishe shi, shi ya ki kallon Inna. Dady ya ce, "To ni na amsa gaisuwarka ba ka gaida uwata ba.? Haidar dai ya yi shiru bai ce komai ba bai kuma kalli Inna ba. Abba ya ce, "Ai yanzu ma shi ya je ya taso ni dole har da kukansa shi fa sai an nemo masa matarsa jawahir. Tun sallar la'asar ya tashi daga office ya je ya sani a gaba ga shi har bayan issha ya ki tafiya gidansa shine na ce ya zo mu je wajenka ko za a sami wani dan labari." Inna ta ce, "Daman abin da ni ma ya kawo ni kenan na zo a karbo min takardar sakin jikata ita ma ta je ta auri wanda take so." Haidar ya yi saurin tasowa ya rike kafar Inna don Allah don Annabi Inna ina jawahir take.? Ta ce, "Ina ruwanka da inda take ba kayi aurenka ba, to ka ba ta takardarta ita ma ta auri wanda take so." Haidar ya ce, "Don Allah don Annabi Inna ki yi hakuri ki yi min rai ki dawo min da matata wallahi zan kula da ita ba za a kuma samun kuskure ba. "Inna ta ce, "A'a, ka je dai ka rike matarka ita ma sai ta samu wani. Haidar ya ce, "Ki rufamin asiri "Inna wallahi ko cewa kika yi sai na saki Kausar za ki dawo min da jawahir sai na sake ta, don ni jawahir ta fiye min kowace mace. "Inna ta ce, "Ni da kake fushi da ni ba ka kula ni. Ya yi saurin cewa, "To yi hakuri mu shirya don Allah Inna jawahir tana ina.? Inna ta ce, "Jawahir tana Abuja gidan kawunku tun washegarin ranar da ka koro ta daga gidanka na tura ta can. "Tuni Haidar ya mike ya nufi bakin kofar waje. Abbansa ya ce, "Haidar ina za ka ne? Ya ce, "Abba Abuja zan tafi yanzu." Dady ya ce, "Ba ka da hankali ne ka dubi lokaci fa yanxu karfe tara ka baro matarka a gida ba ka gudun hakkinta, ka yi hakuri ka koma gidan na yi wa kawun naku waya gobe za su taho a jirgi insha Allahu a gobe za a dawo maka da matarka." Ya rissuna ya karayi musu godiya sannan ya tafi gidansa cike da nishadi. Daga nan su ma suka gama tattaunawa a tsakaninsu Inna direbanta ya maidata gida. Abba ma ya nufi nasa gidan. Washegari sha biyu na rana a Kano ta yi wa Ankul da Aunty da jawahir da ma tun goma na safe kannan Momy suka tafi gidan Haidar don wankewa jawahir kayanta tare da kade mata kura suka share mata sashinta suka gyara komai. Dady da Momy sun yi mamakin ganin yanda jawahir ta girma haka ta kara kyau da haske kamar ba ita ba. Yaya Abba dai da Nasir sai da suka yaba kyan nata. Da yake Inna ma ta zo nan dai aka hadu da Inna da Ankul da Dady da Momi da Anti Maryam a ka yi ta yi wa jawahir fada da nasiha yanda za ta zauna da mijinta da kishiyarta lafiya, ki ci gaba da yi wa mijinki ladabi da biyayya kada ki yarda wata rigima ta kuma hada ku da mijinki sai mun saba miki. Gaba daya kuma suka yi ta sama ta albarka. Anti Maryam ta ja ta daki ta dada yi mata bayanin yanda za ta yi amfani da magangunnan da ta hada mata. Da magariba suka raka ta gidan mijinta kamar sabuwar Amarya. An dai sake yi mata fada da nasiha daga nan kowa ya fashe ya barta. Ta shige sashenta ta kuwa garkame kofa sai karfe goma na dare Haidar ya shigo gidan. Dakin Kausar ya shiga ya same ta a mimmike a gado ya zauna a gefenta ya tambaye ta jawahir kuwa ta dawo? Ta ya mutse fuska tare da tabe baki kai da ka je ka dawo da ita ba ka san ta dawo ko ba ta dawo ba bare ni da ban san ta ba, ko na taba ganin ta ne? Be kuma ce mata komai ba ya yi tolet don inda sabo ya saba da rashin ladabi na Kausar. Da ya gama shirnsa ya nufi dakin jawahir sai ya ji shi a kulle sai ya haye samansa ya yi dai-dai a gadon bacci. Har ya fara bacci ya ji shigowar Kausar ta bi shi gadon suka kwanta. Da safe jawahir ta riga su tashi don haka ta hada birek dinta iya wanda za ta ci ta gyara babban falon nan da dakunanta kamar yadda ta saba ta turare su kamshi ya wadaci ko ina ta shiga ta tsala wankanta da kwalliyarta 'yar ubansu. Shadda ganila ta saka wadda ta sha dinkin surfani duk bulu da yalow da yake kwambineshin ce, ta sha a don gwal fuskar nan tata sai sheki take tana shainin. Ta zama cikakkiyar mace sosai kirjinta kamar ya fashe don cika. Jikinta kuwa wani fitunan nan kamshi ne yake tashi kamar an yi barin turare a jikinta. Ta fito falonta ta zauna, ba babban falo ba. Ta dauki break dinta za ta fara ci kenan ta jiyo taku an yo sashenta. Haidar har ya tashi ya yi wanka ya gama shirnsa cikin kayatacciyar shiga ta alfarma kamai yanda ya saba, amma gimbiya Kausar ana gado a kwance ana ta sharar bacci. ((((((SALON SO)))))) ((((((PART 25))))))) : BY SULAIMAN BOMBOY. . Yana saukowa babban falon ya ji fitinan nan kamshi jawahir mai har gitsa masa kwalkwalwa ya yi hamdala ga ubangiji yayi godiya ga Allah da jawahir ta dawo hannunsa Bai ganta a babban falon ba don haka ya yi sallama a nata falon ya tura kofar ya shiga. "Subhanallahi! Tsarki ya tabbata ga wanda ya hallici wannan kyakyyawar budurwar yarinya sai ka ce balarabiya. Anya ba aljanu ne suke yaudararsa suna neman bude masa ido ba.? "Me ya sa kika tafi wani wajen ba da izinin mijinki ba har tsawon shekara daya? Kina ganin kinyi dai dai kenan? Ko kin manta aure kike yi? Ya za ki da dumbin zunubin tashin hankalin da kika sa mijinki a ciki.?" Ta marairaice fuska kamar za ta yi kuka don Allah yaya kayi hakuri ba zan sake ba. Ya ce, "Shikenan ba wani abu sai dai ki kiyaye gaba. Kin ga yanzu ba mu kadai ne a gidan ba kina tare da abokiyar zama don haka ki kiyaye kin san ba na son hayaniya bare abin da zai daga min hankali. Shiru ta yi ba ta ce komai ba don ta san idan ta yi magana hawaye ne zai zubo don wani dunkulallen abu da ya tokare mata makogaro, ni na san ba komai ba ne sai kishi. Ya ce, "Ba ni break din na ci, "Ta mike tsam ta kai masa gabansa ta durkusa tana hada masa shayin ya yi kauri da madara, bonbita, neskofi, da sauransu. Ta bude masa fulas din soyayyen dankali ne da wainar kwai, sai gasasshiyar kaza da ta gasa. Ya ce, "Je ki falo na ki dauko biredi. "Ta dan yi dum ya ce, "Ba ki ji ba ne? Ta ce, "Yaya matarka fa tana saman? Yace, "Ba komai je ki, ki dauko min ai bacci take yi. Haka ta tafi kamar wadda kwai ya fashewa a ciki shi dai yana tsananin kaunar jawahir yarinya me tsananin hankali da biyayya ga saukin kai ga kuma uwa uba ta hada komai da yake tsananin SO a jikin mace. Jawahir dai har ta hau sama ta sauko ba ta ga matarsa ba. Ta shigo falon ta da siririyar sallamarta ya amsa mata ta zo gabansa ta durkusa ta miko masa, ya ce, "To zauna mu sha ta girgiza kai, ya hada kai tare da cewar ba na son gardama zauna mu sha. Ta zauna suka fara birek Haidar danna birek dinsa yake yi yana ci sosai don yaushe rabon da ya yi break ma a gidansa tun jawahir tana nan. Ita kuwa a yangace ta ke ci kamar mai cin magani ya kalle ta ya ce, "Ke ba za ki bude baki ki ci ba ne? Wato kin fa dawo za ki rinka kin cin abinci ki kuma ramewa ko? Can da yake suna tursasa ki ki ci ai ga shi nan kin yi kiba to ni ma na daina kyale ki dole na matsa miki ki ci ki koshi. Haka ya takura ta ta ci da yawa. Daga nan ya fita ya tafi office cikinsa da koshi. Jawahir kuwa ta rufe kofar falonta ta yi zamanta a dakinta. Dan haka ba ta san wainar da suke toyawa ba. Da ta ji yunwa ragowar birek dinsu na safe ta dauka ta ci ragowar kazar da Yogourt roba biyu ta ji ta koshi kuwa. Shi kuwa Haidar a office duk ya kasa samun sukuni ganin yanda jawahir ta koma. Karfe shida ya tashi daga office ya yi gida. Ya yi sallama falon shiru ba kowa bare a amsa masa. Ya haye samansa ya tube ya yi wanka ya dauro alwala ya yi sallar magariba ya sako kananan kaya ya sauko kasa ya shiga dakin Kausar. Tana tare da 'yan aikinta suna aikin bautarsu na matsa mata kafa wannan abu yana konawa Haidar rai. Suka yi gaggawar fita daga dakin. Ya zauna tare da cewar, "Ina abincina.? Ta ce, "Na ga ba ka cin abincin masu aiki shi ya sa ban ajiye maka ba, ya ce, "Okey kin kyauta. "Ya mike ya fice kawai ya shiga dakin jawahir shiru sai dai ya ji motsin ruwa a bandaki wanka take kenan, don haka ya nemi gefen gadonta ya kishingida yana shakar daddadan kamshin da dakin ya ke yi. Jawahir da ba ta san da mutum a dakin ba ta gama wankanta ta dauko tawul iya gwiwa ta fito gashin kanta duk ya bazu ya manmanne mata a fuska ta bude kofar tolet din ta fito. Tana 'yar wakarta ta nufi gaban mudubi. Subhanallahi! Ai tuni hankalin Haidar ya so gushewa don ganin kyakkyawar kirar jawahir, jiki mulmul da shi ga shi jajir santsi yake yi da sheki, santala santalan cinyoyinta kamar na Baturiya. Ta zauna gaban mudubi ta fito da mayukanta da hadin turarukanta ta fara mulke jikinta. Sam ba ta kula da wani a dakin ba tana shirin yaye tawhul din don shafe jikinta sai ta hango kamar mutum ta mudubin tuni ta razana ta yu kara cikin dimautacciyar murya da takaicin rashin kwancewar tawul din ta ya ce, "A'a jawar meye haka? Ta ce, "To Yaya ai tsoro na ji ban san ka shigo ba, ya ce, "Okey sorry, sorry je ki ki gama shirinki. To kuma sai ta kasa shirin a gabansa sai daya dakin ta shiga ta karasa shirinta ta fito cikin doguwar riga. Tsarki ya tabbata ga Allah, wannan yarinya da kyau take ga iya diresin kamar aljana. Abun da Haidar yake fada kenan a zuciyarsa. Har ta zo gabansa ta durkusa ta ce, "Sannu da zuwa yaya." Ya ce, "Yauwa jawahir kin ci abinci? Ta girgiza kai ya ce, "To me kika ci.? Ta ce, "Yogourt da ragowar naman daxu. Ya ce, "Shi ne zai rike miki ciki? Me ya sa kike son sakaci da cikinki ne? Me ya sa baki girka kin ci ba.?" Ta ce, "Ai gani na yi ba ni kadai ce a gidan ba. To in ban da abinki jawahir ke da gidanki sai an girka an ba ki? Ke da na san ki da kyankyami, za ki rinka cin abincin me aiki ne?" Ta girgiza kanta, ya ce, To kin gani ki rinka girkinki kina ci kin ji ko. Yanzu me za ki ci, ko za mu fita muje mu sayo wani abin ne ko kuma mu je gidan abinci. Ta girgiza kai, "A'a zan girka wani abu yanxu Ya dube ta ya ce, "Dare be yi miki ba. Ta ce, "A'a ba komai. Tun da ta soma magana yake jin wani abu, zil-zil yana tsarga masa don jin dadin muryarta da shaukin begenta. Ya mike ya fita jikinsa a sanyaye kamar wanda kwai ya fashewa a ciki ya fito ya hau samansa sai ya tarar da Kausar a kwance a kan gadonsa tana nishi. Ya isa kusa da ita da saurinsa ya ce, "Lafiya?" Menene ya faru? Ba yanzu na barki a dakinki ba. Ta ce, "Wallahi fama nake yi da ciwon mara tun safe daurewa kawai na ke yi ka daure ka kaini asibiti yanzu." Haidar ya ce, "Yanzu ya dace mu fita asibiti mu bar jawahir ita kadai a gidan? Kausar ta ce, "Haba Haidar me yake damunka ne me zai same ta, ba ga masu aiki nan a gidan ba, ko ka fi so ni na kwana ina murkususu?" Ya ce, "To shikena tashi muje. Lokacin da suka fito don tafiya sannan jawahir ta fito falon za ta shiga kicin wannan shi ne karo na farko da jawahir ta ga Kausar ita ma Kausar ta ganta. Ba su yiwa juna magana ba sai Haidar da ya ce zamu fita yanzu zamu dawo. Jawahir ta shiga kicin kamar ba ta ji me yake cewa ba, suka fice jawahir ta zauna a babban falo ta kunna kallo, salkamar da taji ce ta sata saurin juyowa. "Lalala Bilki yau ke ce a gari?" Gaskiya ba ki da alkawari, ni na za ta ma kin manta da ni." Bilki ta ce, "Haba jawahir ya zan yi na manta da ke, kin san tun ranar da muka zo nan gidan Haidar ya kore mu nake jin tsoron kada nazo na jawo miki wata fitinar. To sai da na ji labarin aurensa na so na zo sai na ji tsoron kada ya cire min kafa daya shi ya sa na hakura na fasa zuwa. Jawahir ta ce, "Yanzu ya aka yi kika zo? "Uhm ke dai bari, tare muke da direba munje gidan kawar Hajiyarmu kusa da ku ne na ga ba zan iya wuce gidanki ba. Jawahir tayi murmushi, "Amma gaskiya na gode na kuma ji dadin zuwanki, don akwai labari da labarai ma sai dai ga shi dare ne da za ki daure da kin zo min da rana mun wuni muna hira. Bilki tayi ajiyar zuciya ta ce, "Kina ganin in na zo babu wata matsala ko Haidar yana nan." Jawahir ta ce, "Ba komai wallahi ba zai ce miki komai ba. To shi kenan jawahir na fita kin ga dare ya yi sai na zo din "Okey Bilki na gode don Allah ina sa ido kada fa ki ki xuwa." "Insha Allahu zan zo" Tayi sallama ta tafi. Jawahir ta soya indomie da kwai ta gasa masa kifi ta hada masa lemon kwakwa da madara ta zuba a jug ta cilla masa kankara ciki ta jere komai a kan tebir din falon ta shiga sashenta ta ci na ta ta watsa ruwa ta wanke bakinta ta je ta yi kwanciyarta. Sai goma na dare su Haidar suka dawo. Kausar ta wuce dakinta Haidar kuwa ya nufi tebur din da abinci yake don yunwar da yake ji tun break din safe da ya yi a dakin jawahir. Ya bude komai ya ci ya yi kat, ya rinka shan lemon kwakwar nan yana nishadi a kasan zuciyarsa kuwa sai shiwa jawahir albarka yake. Da ya gama ya murda kofar dakinta yau ma a rufe gam, ya koma dakinsa yau ma ya kwanta yana murkususu da ya rufe idonsa kyakkyawar surar jawahir yake gani. Ga wata muguwar sha'awarta da tayi masa mugun kamu haka ya rinka juyi yana murkususu. Sai da asuba ya tashi ya yi alwala ya yi Raka'atainil Fajri ya yi ta karatun Alkur'ani ya yi addu'arsa ya shafa. Ya dade yana lazimi sannan ya sauko falon kasa ya zauna ko zai ga jawahir ta fito ya samu ya ganta ko zuciyarsa ta lafa da tsananin radadin kaunarta. Ya yi sa'a kuwa ta bude kofarta ta fito tana sanye da abaya da karamin farin hijab, da ya sha adon bakin les, tana rike da carbi a hannunta ta yi kyau kamar ita ta yi kanta. Duk motsin da tayi sai komai na jikinta ya motsa. Yanda jikinta yake girgiza shi yake dada motsawa da Haidar sha'awarta. Jawahir ta yi mamakin ganinshi a falon, don haka ta karasa gabansa tayi saurin xubewa ta gaisheshi. Ta mike ta nufi kicin idonsa na kanta. Ya ce, "Jawahir" Ta tsaya ba tare da ta juyo ba, ya ce, "Don Allah idan break za ki hada ki hada da mu."(HMMM GASKIYA JAWAHIR AKWAI HAKURI DON NA TABBATA A IRIN KISHI NA MATA BA KOWACCE XATA IYA GIRKI TA BAWA KISHIYAR DA ITA BA XATA YI BA). (((((((SALON SO)))))) : (((((PART 26)))))) : BY SULAIMAN BOMBOY. . Ta yi dan dum kamar ba za ta yi magana ba sannan ta ce, "Kai da wa?" Ya ce, "Ni da Kausar" Ta ce, "Ko a musulunci dakin da ka kwana nan ne yake da hakkin yi maka abinci. To amma tun da hakan ba ta samu ba ni ya zama dole na hada maka, amma ita kuwa wadda ka ambata ban ga dalilin da zan girka mata wani abu na ba ta ba, don ba zamanta na ke yi ba, kuma ni na ajiyeta ba. Kafin ya ce, wani abu ta juya tayi komawarta dakin. Jawahir bata fasa hada break din ba don idan tayi kamar za tayi fushi sai ta tuno abubuwan da Anti Maryam ta gaya mata to sai ta daure tayi ko ba komai yanzu tana ganin nasara don kulawar da Haidar yake yi mata ba kaman a farkon aurensu ba. A babban falon ta shirya masa komai ta koma daki ta tsala wanka ta yi kwalliya ta gani a fada da wani tsadadden material ta yi kyau har ta gaji da kyan, ta sha adon gwala-gwalai kamar ka sace ka gudu. Kamshi ne yake tashi a kowacce kafa ta jikinta. Ta fito falon Haidar yana bisa tebir yana break shi ma ya sha tsantsarerren adonsa da shiga ta alfarma. Yana hango jawahir ya fara sambatu a zuciyarsa, "Subhanallahi! Tsarki ya tabbata ga wanda ya yi kyakyyawar halittar yarinyar nan, ko yaushe zan ga fuskar da zan latsa jikin yarunyar nan, har na gani gado daya da ita? Kai wannan rana da na suma dan dadi Tina daya daga cikin 'yan aikin Kausar ne ta zo ta kama kafar benen Haidar za ta hau, jawahir kuma sannan ta fito daga sashenta shi ne ta doka mata tsawa, "Ke zo nan Tina ta taho jikinta na rawa ta durkusa kasa a gabanta, jawahir ta ce, "Uban wa ya ba ki ikon hawa benen nan? Ko dakin sa'anki ne a ciki? Me za ki yo? Wa ya aike ki? Tina ta ce, Anti ce ta ce na hau na share. Jawahir ta ce, "Wacece Anti?" Tina ta ce Kausar Jawahir ta ce, "Ke dabbar ina ce ko na ce mahaukaciyar ina ce da za ki zo ki haye dakin megida? Ko ku hudu aka auro ne ban sani ba? Tina ta girgiza kai, "To wallahi ki sani wannan ya zamo na farko na karshe ko falon nan kada na kuma ganin dayar ku ta zauna a ciki, da kun shigo ku yi wajen uwar dakinku ko kuma ku yi zamanku can bangaren masu aiki don ni ba zan yarda da kwashe kwashe da tarkace ba. Tina ta ce, "Ki yi hakuri Anti zan kiyaye gaba." Jawahir ta ce, "A'a ni ba Antinku ba ce, ga Antinku can wadda ta kwaso ku ta zo ta zube ku. Ya kamata a ce kuna gidan mazajenku kuna bautar aure amma ga shi kuna zaune kuna bautawa wata katuwar banza, don kwadayi, wato kun fi kwadayin abun duniya da rahamar Ubangiji ko? Tina ta girgiza kai, jawahir ta ce "To ki gayawa ragowar 'yan uwanki ku yi kokari ku fito da mazaje a yi muku aure ku je can ku samu 'yancin kanku ku yi wa Allah bauta. Tina ta rissina tana cewa, "Mun gode Anti insha Allahu za mu gabatar da masoyanmu. Jawahir ta yi mata izinin tafiya ta fita. Haidar yana zaune yana jin su ko ba komai zuciyarsa ta yi dadi da kalaman da ya ji jawahir tana yi yana alfahari da hankalinta. Gefe daya kuma yana tunanin ko dai jawahir ta fara son sa ne don ya ga kamar tana kishinsa, to Allah ya sa haka ne. Kausar ta bude kofar sashenta ta fito tana yamutsa fuska ta dokawa jawahir harara ta nufi wajen Haidar tana yamutsar fuska irin ta marasa lafiya ta ce, "Darling cikina fa ya ki daina ciwon kuma sai na rinka jin kamar yana harbawa ko cikin wata biyu yana fara motsi ne? Haidar ya kamo ta ya zaunar da ita kan cinyarsa, "Kausar kada fa ki wahalar min da baby, ba kya son cin abincin ne yunwa ce take sa shi motsin dole bude bakinki na ba ki, ki ce. Ta bude ya zuba mata, "Yauwa kausar ko ke fa ai gwanda ki ci. Jawahir ta ji wani katutun bakin ciki da kishi ya tokare mata makoshi, lallai ma tsanar da mutumin nan yake yi min ta kai tsana, duk tsawon lokacin da na dauka a gidansa ya kasa kusantata amma daga zuwan wata har ya ba ta ciki, wallahi ba zan yarda ba sai dai a yi wacce za ayi." Ta nufi gun su gadan-gadan a lokacin da Haidar ya sa mata cinyar kaza ke nan a baki jawahir ta tankwabe tare da dankar wuyan Kausar ta ce, "Wallahi sai ta yi amansa, ai ni ba baiwarta ba ce da zan yi mata girki ta zo tana ci." Haidar yayi yayi ta sake ta taki shi kuwa ya fitar da hannu ya shara mata mari. Jawahir ta yi saurin cika Kausar yayin da ta dafe kuncinta zafin marin ya gigita ta inda ta rarumi faramtin tangaran me nauyi ta kwadawa Haidar a gabansa tuni Haidar ya dafe wajen ya kwalla kara ya zube kasa. Hankalin jawahir ya yi mutukar tashi da ganin halin da Haidar yake ciki sai ta sa kuka na shiga uku yaya, Yaya don Allah kayi hakuri wallahi ba da sanina na yi maka ba, Yaya ka yi hakuri ka tashi na tuba na daina ba zan sake ba. Kausar kuwa kofa ta nufa ta kirawo megadi da yaron gidan suka kama shi suka sa shi a mota ta shiga ta tuka motar suka tafi asibiti. Aka kama shi aka shigar da shi daki suka tsayar da Kausar a waje can likitan ya fito ya ce ta je ta nemo dan uwansa namiji. Kausar ta mike ta shiga motarta ta yi gidansu Haidar. Ta yi salllama falon inda ta samu Abbansa da Anti ta durkusa ta gaishe su ta ce, "Daman Haidar ne ba shi da lafiya har an kwantar da shi a asibiti shi ne na zo na fada Cikin hanzari Abba ya mike ko direba bai jira ba ya fita ya hau motarsa ya tafi inda Kausar ta shiga tata motar ta rufa masa baya. Anti ta ce mata, "Duk halin da ake ciki ta yo mata waya ta gaya mata. Ta ce to. Lokacin da su Abba suka isa sannan Haidar yana bacci don haka Abban ya wuce office din Doctor, likita ya mike tsaye ya mikawa Abban hannu suka gaisa, sannan suka zauna. Likita ya ce, "Daman Alhaji larurar da take damun Haidar ce abin babba ne. Cikin firgita da dimauta Abban ya ce, "Me ya same shi? Likitan ya ce, "To dai a bincikenmu mun gano buguwa ce mai tsanani ya yi a gabansa wadda har ta jawo masa mutuwar gabansa, don ba shi da wani kuzari da zai iya kusantar mace bare ya iya biya mata bukatarta. Abban ya dafe kai tare da fadin, "Innalillahi wa inna ilaihir raji'un, yanzu shi kenan dana ya nakasa? Likita me ya jawo masa buguwar.? Likitan ya ce, "Kada ka damu Alhaji za mu yi bakin kokarinmu na ganin ya samu lafiya ya dawo normal. Abba ya yi masa godiya ya koma dakin da Haidar ya ke ya zuba masa ido yana bacci. Jawahir kuwa tun bayan tafiyarsu Haidar asibiti ta kasa samun sukuni sai kuka take yi tana tunanin a wane hali Haidar yake yanzu, ta kasa samun sukunin zuciyarta. Kawarta Bilki ta yi sallama ta shigo, "A'a lafiya jawahir na ganki haka? Jawahir ta ce, "Kyale ni Bilki na bi ta dokin zuciya na aikata abin da zai dame ni. "Me yake faruwa ne?" Jawahir ta kwashe komai ta gaya mata. Bilki ta ce, "Wallahi ba ki kyauta ba, don yanzu Haidar son ki yake yi sosai da kin sani ba ki yi masa wannan dibar albarkar ba, don ba mutunci ba ne mace ta kai hannu kan mijinta da niyyar duka. Tace, "Uhm kyale ni Bilki zafin marin ne ya gigita ni ban san lokacin da na kwada masa ba, karar da ya yi ce ma ta dawo da ni hayyacina." Bilkisu ta ce, "Yanzu ba surutu za ki tsaya ba tashi mu je asibitin ki ga yanda jikin nasa yake. Ta ce, "Kai anya kuwa na je?" Ta ce, "Kwarai ma kuwa, ai tashi kawai mu tafi. "To ai ban san asibitin da ta tafi kai shi ba. "To bari na gano idan direban ya dawo sai mu tambaye shi wanne asibitin ne, ta yi waje. A can asibiti kuwa Abba ya koma gida Kausar tana waje, Haidar ya farka Faruk ya gani a gefen gadonsa a zaune, Faruk ya ce masa, "Sunnu ya kake jin jikin naka? Ya ce, "To da sauki zan ce, "Haidar ya yi tsu can ya ce Faruk ina jawahir?" Cikin mamaki Faruk din ya ce, "Me za ka yi mata? Haidar ya ce, "So nake na san halin da take ciki." "Me ya same ta?" In ji Faruk, Haidar ya kwashe yanda abin ya faru ya gaya masa, Faruk ya ce, haba Haidar me ya sa za ka mare ta? Ai kai ma ba ka yi dai-dai ba. Wallahi yanxu jawahir tana tsananin son ka tun da take yi maka duk abin da kake so, kuma take tsananin gudun bacin ranka, ga shi har ta kasa jure kishinta ta nuna karara. Haidar ka rage zafin zuciya in ba haka ba wata ran zai kai ka ya baro ka. Haidar ya ce, "Ai yanxu ya ma kai ni ya baro din, ni dai don Allah so nake yi ka je gidan ka gano min halin da take ciki inda hali ma don Allah ka rarrashe ta ku taho tare." ♥♥♥SALON SO♥♥♥ ♡♡♡♡27 ♡♡♡♡ . BY SULAIMAN BOMBOY . Faruk ya ce, "Ba ruwana babu inda za ni bare ta zo ka ci mata mutunci ta zo ta rinka ganin h rashin kirkina. Haidar ya ce, "To ni ka kai ni wajen ta na ganta, Faruk ya yi murmushi, Haidar ko dai ka so ma son ta ne?" Haidar ya rintse ido ya ce, "Wallahi ban san lokacin da son yarinyar nan ya yi min dirar mikiya ba, ya shige ni. Inna kwanta da daddare Allah Allah nake gari ya waye don na ga kyakkyawar fuskar matata kuma kanwata, wallahi ni kadai na san yanda tsananin son jawahir yake raina, kai abin da na yi wa Kausar a gananta ma na yi ne don na auna na ga tana so na kuwa ko ni kadai nake shirme na. Faruk ya ce, Ka ga irin abin da na so ka gane tuntuni ka ki, to yanzu kuwa in ta ji halin da kake ciki sai ta ce don ka ga ba za iya kwanciya da ita ba ne, shi yasa ka nemi shiri da ita. Haidar ya ce, "Ai likita ya ce zan warke fa". Ko da yake yanzu ne lokacin tantance wanda take sonka don Allah da wadda a kayi auren sha awa. "Haidar ya ce, Ni dai don Allah ka je ka taho min da sahibata ko don na ga halin da take ciki. Faruk ya ce, "Zan je ai yanxu Kausar ta turo kofar ta shiga fuskarta a murtuke babu alamar fara'a, ta je gefe daya ta zauna ba tare da ta kula wani a cikinsu ba. Faruk ya mike Haidar bari na je in dawo ko? Duk yanda muka yi zan zo ka ji. Ya ce, "Don Allah ka je fa yanzu kada ka ki zuwa ka ji. Faruk ya ce Insha Allahu kuwa yanzu zan je. Faruk ya fita ya bar su Haidar ya juya ya kalli Kausar ya ce, "Me ya same ki ne na ga kamar ranki a ba ce? Ko cikinne yake ciwo?" Ta zumbura baki, "Kai yanzu har ka manta da barnar da Jawahir ta yi maka a jikinka har kake cewa a je a taho da ita? To wallahi ni ba zan yarda ba don ta ga ita ba ta da amfani a wajenka shine za ta nakasta min kai, wato ka zamo marar amfani, to wallahi ba zan yarda ba don ita ma sai na nakasta ta, sai dai duk abin da za a yi a yi." Haidar ya daka mata tsawa ya ce, "Ke ki shiga hankalinki kina ganin duk da son da nake wa jawahir da ta yi miki abu sai da na yi mata marin da ta gigice, to wallahi ki shiga hankalinki idan kika sake kika taba min mata wallahi sai kin yi mugun raina kanki, don sai kin yi mamakin abin da zan yi miki." Ta mike ta yi waje tana kunkuni ta zari mota ta nufi gidan Yakumbon Haidar wato kakarsa ta wajen uba, ta je ta zayyane mata maganganun karya da gaskiya ta gaya mata, Yakumbo ta hau sababi ka ji mu da tsinanniyar yarinya don ba ta son sa shine take neman hanyar kashe shi, to wallahi bi ba yarda zan yi ba, tashi ki koma asibitin gani nan zuwa yanzun nan, "Kausar ta koma asibiti ta tarar su Anti da Momy da su Yaya Abba sun cika asibitin taf, ana ta jajen abin da ya faru. Shi kuwa Faruk da ya je gidan Haidar yayi sallama falon, su jawahir suna daga kicin suka amsa sallamar suka fito falon, Faruk ya nemi waje ya zauna jawahir da Bilkisu suka gaishe shi, faruk ya ce, Haidar ne ya turo ni na zo na ga halin da kike ciki in kuma da hali ki zo mu je yana son ganinki. "Jawahir ta sunkuyar da kai ta ce, "Gaskiya Yaya Faruk ba zan je inda yaya yake ba, don in na je ban san irin wulakancin da zai yi min ba, ka ga kuwa da na je ya bata min rai ai gwara ban je ba. Faruk ya ce, "Wallahi Haidar yana wani hali na mutuwar sonki kin san miskilancinsa ya rasa ta hanyar da zai bi ya nuna miki Kaunar da yake miki don yanzu da kin ga irin magiyar da lallamin da ya rinka yi min sai na zo gare ki dakin tausaya masa. Kafin ta yi magana Bilki ta ce, "Faruk bari mu karasa girkin da za mu kai masa sai mu fito mu je." ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** Faruk ya ce, to shi kenan bari na je na dawo. Bilki ta zuzzuba komai a fulas ita kuma jawahir ta je ta shiga wanka ta fito ta shirya cikin atamfa ja! Super Holland dinkin filet ne ya kama jikinta sai zani da dankwali da ta daura, farar hoda kawai ta shafa a fuskarta sai dan man leben da ta shafa ta dauko jan mayafi da jan takalmi ta saka, kunnanta fashon din yari ne me jan dutse a tsakiya. Bilkisu ta tafa mata "Amma yarinyar nan kin yi kyau, kwalliyar taki ta burge ni sai dai kash kin manta a shafa hadin turarukanki. Jawahir ta yamutsa fuska, "Kin san fa inda za mu je za ki ce na shafa hadin turare. Bilki ta ce, to meye ba wajen mijinki za ki ba, ai gwanda ki shafa turarukan da kamshinsu zai gigitar da shi kuma ga karin lada a wajen Ubangiji, don duk sanda mace ta yi abun da zai farantawa mijinta har ya ji dadi a ransa to Ubangiji zai ba ta ladan da ba ta san adadin yawansa ba. Jawahir ta ce, Haka ne bari na shafa don na fuskace shi yana son kamshi. Sun jejjera fulas-fulas din a dan kwando me kyau ta lullube shi da farin yanki me adon bakin les da fulawoyi a jiki. Faruk ya dawo suka dunguma a motarsa zuwa asibiti. A lokacin ba kowa duk sun tafi sai kausar kawai da take zaune kan kujera tana karanta jarida, ba ta daga kai ba balle ta kalli wani a cikinsu. Faruk ya ce, "To ga ta nan na cika alkawari ko, ga ta na kawo maka Haidar ya yi murmushi ya ce, "Ai kuwa na gode Bilkisu ce ta fara gaishe shi tare da yi masa ya jiki. Cikin fara'a ya ce, "Ai jiki Alhamdullahi." Jawahir ta durkusa cikin dari-dari da rawar murya Kamar mai shirin kuka ta ce, "Yaya ina wuni? Ya jikin? Ya ce, "Lafiya lau jawahir ya naki jikin.? Ya sa hannu ya dago ta daga tsugunnun ya shafi kuncinta, ya ce, "Wai haka kuncinki ya tashi hannuna ya fito radau na marin da na yi miki, sorry Babyna ki gafarce ni, "Kafin tayi magana aka turo kofar aka shigo tare da sallama, Yakwalkwal ce ta shigo rike da hannun Sayyid. Sayyid ya fincike da gudu ya nufi jawahir yana cewa, "Anti na anti na, shine rannan kika gudu unguwa kika bar ni ina ta kiran ki ba ki zo kin tafi da ni ba. "Jawahir ta dauke shi ai yau da kai zan tafi kai ta kwana a can ko? Jawahir ba ta ankara ba ta ji saukar mari a kuncinta, Yagwalgwal ce ta kuma hau fada, "Annamimiya me kuma ya kawo ki wajen jikana kin so ki kashe shi, Allah bai baki nasara ba shi ne kika biyo shi nan ki karasa shi ko? Haidar kuwa tuni ya diro daga gadon jinyar ya tare jawahir yana cewa, "Haba Yagwalgwal ya za ki doke ta ita ma fa ba lafiya ce da ita ba, me ta yi miki?" Yagwalgwal ta ce, "Ubanka ta yi min, shege sallamamme so kake yanda uwarka ta mallake Alhaji kai ma jikan mallake ka za ayi, "Yagwalgwal ta ci gaba da nuna jawahir da dan yatsa tana yi mata sababi, daga yau na gaya miki ba ke ba Haidar in ke mayya ce ki ci kanki da kanki, haka kawai hankalinsa ya kwanta yana zaune da matarsa lafiya za ki zo ki bata musu zama. Jawahir ta mike jikinta ba kwari za ta fita Haidar ya yi saurin riko hannunta yana cewa, "Haba Yagwalgwal ya za ki zo ki korar min matata ki ce sai ta tafi? Ai ba ita ta kawo kanta ba ni na sa a je a dauko ta in ta tafi waye zai yi jiyya ta? Kawai mutum da matarsa a nemi raba su. Kan ya rufe baki bakinsa Yagwalgwal ta ba shi nasa marin ya dafe kunci ita kuma ta ci gaba da sababi tana nuna shi da dan yatsa, "Ka shiga hankalinka ka san da wacce kake magana, idan ba ka san ciwon kanka ba ai ni na san ciwonka, yarinya ta nakasa ka ka zamo marar amfani amma ba za ka guje ta ba, wata rana ma ranka za ta raba ka da shi. Jawahir ta fincike hannunta ta yi waje cikin sauri Haidar ya yunkura zai bi ta Yagwalgwal ta rike shi, Bilkisu ta bi bayan jawahir yayin da Faruk ya rufa musu baya. Da kyar da ban hakuri ya shawo kan jawahir ta shiga motarsa don ya mayar da su gida. Faruk ya ce, "Don Allah don Annabi jawahir ki yi hakuri da abin da tsuhowar nan ta yi miki. Jawahir ta yi saurin katse shi, "Haba yaya Faruk ka fi kowa sanin ta yanda a ka yi aurenmu da yaya, ba son sa nake yi ba na aure shi don biyayyar iyayena na zo nake zaman hakuri da shi, ya tashi ya dankaro min kishiya ni duk hakurin da na yi a kansa ba a gani ba kenan. Fashe da kuka Faruk ya ci gaba da rarrashinta ki yi hakuri jawahir ki tuna aure kike, aure kuwa bautar Ubangiji ne kada bacin ran wasu ya sa ki sabawa megidanki kin ji?" Yanda na san ki da hakuri da ladabi da biyayya ki ci gaba da yi komai me wucewa ne wata rana sai labari kin ji?". . BY SULAIMAN BOMBOY . WHATSAPP . 08038491393 ♥♥♥SALON SO♥♥♥ ♡♡PART 2⃣8⃣♡♡ . By Sulaiman Bomboy . Ta daga kai ya ce, "Yauwa ko ke fa gobe ku shirya da wuri sai na zo na kai ku ta ce to. Ya sauke su a gidan shi kuma ya koma asibitin shi kuwa Haidar tun bayan fitarsu jawahir da Yagwalgwal ta rike shi don kar ya bi su gado ya koma ya kwanta ya yi rigingine ya rufe idonsa. Maganar duniya babu wadda ba a yi masa ba amma ya yi musu shiru ko motsi bai yi ba dole suka gaji suka hakura suka bar masa dakin. Faruk ya shigo ya dinga lallaminsa yana ba shi baki tare da va shi hakuri sannan ya tashi ya jawo kwandon da jawahir ta jero masa kayan abinci. Dakakkiyar sakwara ce lukui da miyar agushi mai wadataccen nama, sai jalof din taliya da lemon kwakwa. Haidar ya ce, "Ka ga yarinyar nan da zan bata mata rai ba za ta ki yin abinci ba don gudun kada ta bar ni da yunwa." Faruk ya ce, ai haka ake so ka ga yanzu sai ka rike ta da kyau ka nuna mata garanci wanda ba ta samu ba a baya. Haidar ya ce, "Allah dai ya ba ni lafiya amin in ji Faruk yayin da ya zuba musu abincin a filet din da ta zubo suka ci sosai dan shi kansa Faruk ya yaba da dadin girkin nata. Can kuwa Bilki ta mike don tafiya gida, "To ni zan tafi jawahir sai dai gobe zan zo da wuri na raka ki mu sake dubo shi. Jawahir ta hangame baki ta ce, "Don kin ji Faruk ya fada ba kya tsoron mu je a yi mana wani sabon wulakancin da ya fi na yau.? Bilkisu ta ce, "Insha Allahu hakan ba za ta faru ba gwanda ki je, kada su samu kafar raba ki da mijinki ga shi kuma yanzu kuna son juna. Jawahir ta ce, "Shi kenan Allah ya kai mu goben na gode Bilki da kaunar da kike min, da ba ni shawarwari masu kyau da kike yi, Allah ya kara mana dankon zumunci a tsakaninmu amin. Da haka suka yi sallama ta tafi. Jawahir ta shiga dakinta ta kwanta tana tunanin abin da ya faru yau da ita. Faruk ya fita ya yi sallar insha Haidar ya kalli Kausar ya ce ke ba za ki yi sallar ba ne na ga ko magariba ba kiyiba? Ta ce, "A'a ina ruwanka a yin sallah ta ka ga malam kawai ka ji da abin da ya dame ka. Faruk ya turo kofar ya shigo Kausar ta zuba masa harara tare da jan tsaki ta mike ta bar dakin. Faruk ya taimakawa Haidar ya yi Sallah, Haidar ya daga hannu sama ya dade yana addu'a sannan ya shafa ya xuba tagumi. Faruk ya cire hannun tagumin ya ce, "Haba malam menene kuma? Ka yi hakuri a kan larurae da ta same ka, ka yarda da kaddara ko? Haidar ya ce, wallahi ba wannan ne ya dame ni ba halin da jawahir rake ciki nake tunani kada fa ta Gudu gidan Inna ta kuma boye ta ka san ranta ya ba ci dazu da abin da Yagwalgwal ta yi mata. Faruk ya ce, "Ba na jin za ta fita har gida na kai ta kuma na babbata hakuri ka san yarinyar akwai biyayya" To don Allah ka je ka taho min da ita ta kwana a wajena ka ga gidan ba kowa sai masu aiki. "Faruk ya ce, "Ka yi hakuri da safe ai za ta zo ka ga yanzu dare ya yi yanxu haka ma ta kwanta. Haidar ya ce, "Haba Faruk don Allah ka taimaka min ka je ka taho min da jawahir yanzu duk girman gidan nan ta kwana ita kadai sai masu aiki? Faruk ya ce, "Shikenan bari na je amma sai na biya na dau Hafsa don ita ma ta zo ganin likita." Haidar ya ce, "Ko dai ta harbu ne.? Faruk ya yi murmushi ya ce, "To ga mu dai ga Allah don mun sa rai. Ya fita yana dariya ya biya ya dauki matarsa Hafsa suka tafi. Ya ce, Ya ku ka yi da likitan? Ta ce, "Gwaje gwaje ya yi min ya kuma dauki fitsarina ya ce da safe a zo a karbi result din. Faruk ya ce, "To Allah ya taimaka mana ya sa abin da muke nema ne, ta ce Amin. Suka yi wa juna murmushi. Suka yi fakin a harabar gidan Hafsa ce a gaba don ita take buga kofar falon nasu da yake kulle. Jawahir da take takure a falo don zuciyarta cike take da tsoro da fargaba ka sancewar ta ita kadai a sashen ta yi tunanin ko ta kirawo 'yan aikin Kausar su taya ta kwana sai kuma ta fasa, to jin bugun sai ya dada tsoratar da ita. A tsorace ta je gaban kofar cikin rawar murya ta ce, "Wanene?" Faruk ya ce, "Bude mu ne, ta kalli agogo karfe tara gabanta ya fadi, Allah ya sa dai lafiya? Ta bude kofar ta ba su hanya suka shigo Faruk ya ce, "Sarkin tsoro da kin zata barayi ne suka zo sa ce ki?" Ta yi dariya ta kamo hannun Hafsa ta ce, "Wai yaushe rabon ki da gidan nan? Ko da yake ban sani ba ko kina zuwa wajen amaryarku Kausar, "Hafsa ta yi dariya ta ce, Ni ina zan zo gidan nan mutuniyata ba ta nan ta gudu ta bar min abokin miji ya zamo abin tausayi a gari?" Ga ba daya suka yi dariya. Faruk ya ce, "Kar dai a gaji da mu dan mun kuma zuwa da kokon bararmu da karin ban hakuri megida ya ce, a zo a tafi dake don Allah ki kwana a wajensa. Ta yi shiru can ta ce gaskiya ni ba zan je wajensa na kwana ba. Faruk ya ce, "Subhanallahi, kin san hukuncin matar da mijinta ya yi kiranta ta ki zuwa kuwa? Ko kina so ki hadu da fushin ubangiji ne? Jawahir ta ce, "Gaskiya Yaya faruk ba zan je ba, ba Kausar tana can ba? Ai ita ta saba kwanciya da shi ni in na je ina da abin da zan yi masa ne? Faruk ya ce, "Haba jawahir kada ki yi haka mana da iliminki da komai ki yi hakuri ki amsa kiran mijinki mana. Ta ce, "Haba yaya Faruk har ka manta irin zaman da na yi da yaya Haidar a gidan nan ni bani da hakki a kansa sai shi yanzu yake da hakki a kaina har zai neme ni?" Ta sa kuka ta mike tayi daki, "Wallahi ba inda zan je". Ta turo kofar dakinta ta kulle. Hafsa ta ce, "Gaskiya fa ni fa ban ga laifin jawahir ba, don gaskiya an zalinceta" Faruk ya dakawa Hafsa tsawa tare da cewa, "Yi min shiru ana neman sasanta magana kina dada tunzurata. Ya jawo wayarsa ya yi danne-danne. Haidar ya dauka, "Hello" Yauwa Haidar ka kwantar da hankalinka kayi hakuri mun zo mun tarar jawahir tayi bacci amma don Allah kada ka tsayar da hankalinka da safe kafin na tafi office zan biya na dauko maka ita. Haidar kafin ya ce, wani abu tuni Faruk ya katse wayar ya kuma kasheta gaba daya don ya san halin Haidar ba kyale shi zai yi ba. Haidar kuwa tun daga lokacin wata zuffa ta rinka tsiyayo masa, hankalinsa ya yi mummunan tashi, jikinsa sai rawar sanyi yake yi. Ba jimawa zazzabi mai zafi ya rufe shi. Nan da nan jiki ya rikice a ranar da sai Abbansa ne da yaya Abba suka kwana a wajensa. Ba shi da wata magana sai ta ambaton an bar jawahir ita kadai a gidan nan sai masu aiki kada wani abu ya samar masa ita. Yaya Abba ne yake dan karfafa masa gwiwa yana tunasarsa. Yawan ambaton jawahir da Haidar yake yi ya sa Kausar ta yi fushi ta baro asibitin ta dawo gida. Jiyya ta koma hannun yaya Abba da Faruk, amma asibitin kullum cike yake da yan uwa da abokan arziki sai dai rashin matansa a wajen. Duk da haka Yagwalgwal ba ta fasa yada habaici da kananan maganganu ba don haka Anti ba ta son yawan zuwa don ita take yiwa habaicin. Kamar ita ta haifa mata Haidar din Yau kwanan Haidar hudu kenan a asibiti suna zaune a dakin jinyar, Faruk da yaya Abba Haidar ya ce da su, Faruk da yaya Abba ku fara hada kaya ku karbo min takardar sallama." Yaya Abba ya ce, Ah sabo da me? Cikin raunanniyar murya Haidar ya ce, "To kun ki zuwa ku rarraso min jawahir ta zo gareni na ganta ko hankalina ya kwanta. Tun da haka ne gwanda na koma gidan na yi jinyata a can inda zan samu kulawarta. Shi dai yaya Abba ba ya son jawahir ta zo wajen nan ko don sabo da kananan maganganun da Yagwalgwal take yi, don haka ya yi shiru bai ce komai ba. Haidar kawai ya fara hada kaya Faruk ya tausaya masa, ya ce, "Bari Haidar yi hakuri bari na je yanzu na shawo kanta insha Allahu za ta zo. Jawahir tana zaune tana bitar karatun Alkur'ani wayarta ta yi kara. Ta tsagaita da karatun ta dauka, "Hello wa ke magana? Faruk ya ce, "Ni ne daman na bugo na gaya miki Haidar yana cikin dayan biyu ko mutuwa ko rayuwa, don ya rikice an rasa gane kansa sai kiran sunanki kawai yake yi" Jawahir ta gigice, "Na shiga uku yaya faruk yanzu ina yayan yake? "Yana can asibiti a rikice." "Wayyo yaya faruk! Don Allah ka kwantar masa da hankali yanzu zan zo." Ya ce, "Ina harabar gidanku ina jiranki ki fito da hanzari. . Whatsapp 0⃣8⃣0⃣3⃣8⃣4⃣9⃣1⃣3⃣9⃣3⃣ ♥♥♥SALON SO♥♥♥ . ♥♥PART 2⃣9⃣♥♥ . By Sulaiman Bomboy. . Kafin ya rufe bakinsa ya ganta ta fito da wayar kange a kunnenta. Ya bude mata bayan motar ta fada, shi kuma ya shiga gaba ya tuka suka yi gaba. Yana tsayar da motar jawahir ta bude ta fito a guje ta shiga dakin da yake tana danna kai ta tarar da shi a gado yana ta faman ihu. "Wayyo Allah! Ya dafe cikinsa yana ta juyi." Ga shi dakin sai shi kadai ba kowa, nan da nan hankalin jawahir ya tashi, tausayinsa ya kama ta sai kawai hawaye taji yana zubowa daga idannuwanta ta zauna a gefen gadon ta dago kansa ta dora a cinyarta tana rike da shi sai sannan take yi masa, gani take da tana da ikon cire ciwon nan ta dawo da shi jikinta da ta yi domin kawai ya huta a abin da yake damunsa. "Sannu yaya na kirawo likita ya ba ka magani. Wayyo yaya cikinka ne yake ciwo? Yaya ko ina ciwon yake yi? Sannu yaya, bari na hada maka tea ka sha ko? Ko za ka iya cin abincin? Don Allah yaya ka tashi. A hankali nishi ya lafa sai kadan kadan daga can ya yi shiru ciwon ya tafi kenan. Jawahir ta rankwafa kansa, "Sannu yaya". Ya lalubi hannunta ya danke a nasa cikin magana sanyi- sanyi irin wanda yake jin jiki ya ce, "Yaushe kika zo? Ta ce, "Ban dade da zuwa ba. Ina yaya Abban ya tafi ya barka kai kadai?" "Yanzu nan kafin ciwon ya tashi ya tafi gida amma yanzu zai dawo."Ta ce "Amma dai bai kamata su rinka barin ka kai kadai ba kana cikin wannan hali." "To ya zan yi jawahir ke ma da kike 'yar uwata matata kin guje ni kin ki jiyyata waye zai jura?" Jawahir ta ce, "Ka yi hakuri yaya ba wai na ki zama a wajenka bane ka san halin Yagwalgwal kar ta zo tana tsinka na a asibiti shi ya sa. Haidar ya ce, "To shi kenan ba komai zan nemi likita ya ba ni sallama sai mu koma gida na yi jinyar a can ko?" Ta ce, "Haba yaya gwanda ka zauna a nan din ka ga sun fi kulawa." To jawahir ai ba zan juri rashin ganinki ba gwanda dai na koma gidan." Daidai nan likita ya shigo ya dubi Haidar ya ce, yanxu ina ganin za mu sallameka ka koma gida tun da Abbanka ya ce kasar waje zai futa da kai. Don haka ga takardar sallama. Jawahir ta ce, "To likita yawan ciwon cikin da yake fa? Likitan ya ce ba komai wannan mun bashi magunguna sai dai a dinga kula wajen ba shi ya sha." Anan yaya Abba ya shigo ya kalli jawahir ya ce wato sai yau kika ga damar xuwa wajen mijinki ko? Kina sane da ba shi da lafiya yana kwance a asibiti amma ba za ki zauna kusa da shi ba, don taimaka ma sa ba ko.? Jawahir cikin biyayya jawahir ta ce, "Kayi hakuri yaya insha Allahu ba zan sake ba, "Faruk ya shigo suka kwashi kaya da Haidar suka yi gidansa. Dakinsa suka wuce da shi suna budewa kamshi ya bige su ko ina a gyare fes kamar yana nan. Jawahir ta hado musu abubuwan ci da na sha suka ci suka sha suka yi kat, sannan suka yi musu sallama tare da kara yi musu addu'ar samun sauki. Jawahir ta shige tolet dinsa ta hada masa ruwan wanka a baho ta zuba turaren wanka a cikin ruwan nan da nan turirin kamshi ya rinka tashi. Ta fito daga tolet din ta durkusa Yaya ga ruwan wanka can na hada maka, ya ce yauwa Babyna na gode. Ya mike ya shige tolet dinshi kansa kamshin da tolet din yake yi dabanne. Yana shiga cikin ruwan ya ji wani dadin ni'ima ya ratsa shi ya fara wankan. Jawahir kuwa ta fito masa da wasu kananan kaya, wando je three Quarter (tiri kwata) da rigar 50 Cent marar hannu ta kara feshe su da turare. Ta debo masa mayukan da zai yi amfani da su da turarukan. Ta ja masa kofar dakin ta sauka zuwa kasa nata dakin. A lokacin kuma Kausar ta dawo ko daga ina take oho ita ta sani. Jawahir ta shiga wanka ta fito ta gyara jikinta sai zuba kamshi take yi kamar wadda aka yi barin turare a jikinta. Riga da wando ta saka da hula mai harafin sunanta. Fuskar nan tata sai sheki take yi, jikinta sumul-sumul gwanin sha'awa kirjinta ya cika fam, da na shanu. Ta bude kofar ta fito Haidar yana kwance a doguwar kujera da karamin kur'ani a hannunsa yana karatu. Kausar tana kujera me zaman mutum daya tana zaune da jarida a hannunta tana dubawa, kamshin da suka ji ne ya sa su saurin dago kai Kausar ta saki tsaki ta mai da kanta ga karatunta. Jawahir ta wuce kicin ta dauko kofin gilas me kyau ta bude firji ta dauko robar ruwa ta Highland ta iso gaban kuherar da Haidar yake kwance ta zauna a kasa kan kafet ta balle bakin robar ruwan ta tsiyayo ta fiffito da magungunan ta mika masa, "Yaya ga magungunan. Ya dan mike zaune ya karbi magungunan ta watsa bakinsa ta kafa masa kofin a baki ya sha ruwan ya ce ta dan danna masa kafafuwansa don ciwo suke yi masa. Ta mike sannu a hankali ta rinka mamnatsa masa tana yi masa tausa. Jin dadin tausar da ya jine ya sa shi fadin wash, wash a hankali tare da lumshe ido. Ita kuwa Allah sarki sai ce masa take yi sannu sannu yaya cikin alamun ban tausayi, shi kuwa taushin fatar hannunta mai kama da atafa shi yake neman dimautar da shi, har yana neman sa shi ya fita daga hayyacinsa, ba dan yana gudun kada girma ya fadi ba ai da ya rungumota. A ka kwankwasa kofar falon jawahir ta kalli Haidar da yake kwance yana lumshe ido don jin dadin tausa ta ce, "Yaya na je na bude kofar.? Kai kawai ya iya daga mata don maganar ta ki fita kanta bude kofar ta ja da baya don ganin Yagwalgwal ce. Jawahir ta durkusa kasa ta gaishe ta, ta ce "Munafuka ba zan amsa gaisuwar taki ba, me kike jira a gidan da baki tafi ba tun da kiyayyar da kike yi masa har ta kai ki sabauta masa lafiyarsa ai za ki iya kashe shi ma, don haka ni gaskiya ban yarda da wannan auren naku ba ka sake ta kawai na gaya maka ba na son gayyar tsiya gayyar jarabawa. Jawahir ta fashe da kuka ta kalli Haidar ta ce, wallahi ba don na riga na yi wa Dadyna alkawarin ba zan kuma fita daga gidan nan ba, ba tare da izininka ba wallahi yau da na bar zaman gidanka. Ta durkusa a gabansa tana kuka, "Yaya don Allah don Annabi yaya ka taimake ni ka sake ni ko ni ma na samu sukuni a zuciyata. Haidar ya sunkuya ya dago jawahir ya hada ta da kirjinsa ya rungumeta yana shafa bayanta alamar rarrashi, ransa a bace zuciyarsa ta yi bakikkirin sai fat-fat take yi kamar ta fasa kirjinsa ta fito waje. Ya kalli Yagwalgwal ya ce, "Yagwalgwal ina ganin girmanki kada ki bari kimarki ta zube a idona, jawahir 'yar uwata ce ko ba aure a tsakaninmu ni me rike ta ne ballantana matata ta sunna ki rika aibata ta a gabana, ai aurena da jawahir mutu ka raba takalmin kaza. Yagwalgwal ta kama salati tana tafa hannu, "Yanzu dan nan ni kake gayawa haka a kan wannan mai kama da sadakar yallan kake neman zagina, to bari na je wajen uban naka in kai ban isa da kai ba ai shi ba zai ki jin maganata ba, tun da ni na haifeshi ko. Jawahir ta zame jikinta daga jikin Haidar ta nufi dakinta tana kuka ta rufe kofarta. Haidar ya kamo hannun Yagwalgwal ya ce, "Yi hakuri matar ta karfen na san du kishi ne yake dawainiya da ke, Ta doke hannunsa ni sake ni me kuma za ka gaya min bayan ka gama yi min rashin kunya. Ya dada kamo hannunta yi hakuri zo mu je sama dakina na gaya miki komai don ki ji yanda abin yake. Da kyar ya shawo kanta suka hau samansa suka zauna a falonsa, duk wannan abin da ake yi Kausar tana zaune a kujerar da take tana kallonsu kawai ba tare da ta tofa komai ba. Haidar ya ce da Yagwalgwal "Wallahi yarinyar nan jawahir tana da mutukar hakuri ga ladabi da biyayya ga sanin ya kamata da hangen nesa, tana aiki da ilimin da Ubangiji ya ba ta, idan aka ce za a yi ta tafiya a yanda a ke yi yanzu, to hakika hakurin jawahir zai iya kai ni wuta." Yagwalgwal ta ce, "Dakata! Don na ce ka rabu da ita kake kawo min wannan bayanin, ka je kada ka sake ta ran da ta kashe ka ai ma zo mu dauki gawarka ko? Haidar ya ce, "Dole dai sai na fasa miki tarihinmu za ki yarda da zancena. Haidar ya faro mata irin tsanar da ya yi wa jawahir tun daga farko da yanda har a ka yi auren da irin zaman da suka yi da dalilin da ya sa jawahir barin gidansa har kawo yau. Yagwalgwal ta saka salati tana cewa, "Ashe ni balokokon vanza nake yi kai ne marar gaskiya? To wallahi ka kula ka rike 'yar uwarka da kyau don tana yi maka son gaskiya. Da haka dai suka yi sallama ya debo kudi me yawa ya bata ta yi masa godiya tare da sa masa albarka ta ce kuma za ta zo ta bawa jawahir hakuri idan ta wuce. Haidar ya juyo daga rakiyar Yagwalgwal ya murda kofar dakin jawahir ya shiga, kamshin dadi ne suka buge shi ya sheka ya karasa cikin dakin. Tana zaune a gefen gadonta hada kai da gwiwa tana shasshekar kuka, ya zauna a gefen gadon ya dago ta ya kara ta da jikinsa ya rungume ta, "Subhanallahi wannan jiki haka mai taushi da dadin kamshi kamar atufa, Ubangiji ka nuna min ranar da zan mallaki komai na yarinyar nan da na nuna mata tsantsar soyayya da kaunar da ba a taba nunawa wata 'ya mace ba. Duk zancen nan a zuciyarsa yake yi wanda har ya so ya shagala cikin tunanin kyan kirar jawahir. Sautin kukanta ne ya dawo da shi hayyacinsa. Cikin taushin murya da magana kasa-kasa kamar mai rada yake rarrashinta yana dan bubbuga bayanta, "Sorry Babyna yi shiru haka kada kanki ya zo yana ciwo kin ji baby na yi hakuri, ta dada shagwabewa tare da langabewa a jikinsa tana kuka kasa-kasa cikin sigar kissa da shagwaba kukan nata me shiga rai da tsayawa masoyi a zuciya. Tuni kirjin Haidar ya fara bugawa fat fat, "Subhanallahi ya salam wai yaushe zan mallaki wannan tsantaararren jikin mai kama da robar balo-balo? Muryarta ya tsinkaya cikin rauni da taushi da dadin murya tana cewa, "Yaya ka sake ni na koma gida tun da kakarka ba ta son na zauna da kai." Haidar ya ce, "A' uxubillahi kada na kuma jin kin furta wannan kalmar kin ji ko, don ubangiji yana tsinewa duk matar da ta nemi mijinta da ya sake ta, kada bacin rai ya sa ki rinka jawowa kanki fadawa cikin fushin ubangiji kin ji ko? Yi saurin yin istigifari." A hankali ta bude baki ta rinka nanata istigifari, ya ce, "Yauwa Babyna Yagwalgwal ta ce a ba ki hakuri. Zumbur ta mike ta shiga tolet don ba ta son maganar don ita a zatonta tanda Yagwalgwal take tsanarta da nuna mata kiyayya ba za ta taba son ta ba. Haidar kuwa binta ya yi da kallo komai nata sha awa yake ba shi komai na jikinta burge shi ya ke yi, wai shi ya zai yi da wannan zazzafar kaunar da yake yi wa jawahir ne? Ta yaya zai yi ya shawo kanta su kwanta gado daya ne da shi? Duk dai da tanxu ba shi da karfin gaban da zai tabuka mata wani abu to amma ko wasanni da sun yi shi da ya ji ta kwance kan kirjinsa yana wasa da wadannan tantsa-tantsan na shanun nata(nono). Duk dai da shi ya yi wasa da damar da ya samu tun farko. Ya dade a zaune yana zaman jira shiru-shiru jawahir ba ta fito ba dole ya mike ya fita, tana jin fitarsa ta fito ta sawa kofarta mukulli. . . WHATSAPP. 0⃣8⃣0⃣3⃣8⃣4⃣9⃣1⃣3⃣9⃣3⃣ ♥♥♥SALON SO♥♥♥ ♥♥PART 3⃣0⃣♥♥ . By Sulaiman Bomboy. . Abu wasa-wasa jawahir ta kwana ta wuni ba tare da ta fito Haidar ya ganta ba ko ta yi saken kofarta a bude ya shigo. Sai dai wani abin mamaki da safe za ta hada masa lafiyayyen break a kicin din wajenta sai ta leko falon ta ga ba kowa sannan ta jere masa kayan break din ta kuma ajiye masa maganin da zai sha na lokacin da robar ruwan Highland ta koma bangarenta ta kulle kofarta, sai dai in Haidar ya gama shirnsa ya sauko kasa ya hau tebir ya yi break ya dauki magani ya sha ya jira ko jawahir za ta bude ya ji shiru ya taba kofarta ya ji ta a kulle. A lokacin ya juya ya koma sama sannan ya tashi 'yar mulkin tasa wato kausar sarkin 'yan hutu, to wani abin mamakin duk da yau kusan a falo ya wuni amma be ga jawahir ta fito ba bare ya kalli idonta ya ga yanda ta kwana. Sai da ya ji an yi kiran sallar azahar ya daura alwalla ya fita masallaci amma kafin ya dawo jawahir ta fito ta jere masa kayan abinci, tuwon farar shinkafa ya tuku ya yi mulmul da shi da miyar agushi, wadda don dahuwa kazar da take ciki duk ta narke ta dagargaje a ciki. Ta gasa masa naman rago mai ruwa ruwa ya sha kayan kamshi ga tumatir da albasa kai dai kamshi yake tashi. Sai lemon aya da ta hadawa kanta ta zuba masa a jek ta cilla kankara ya sha kayan kamshi, ta jere komai cikin kayatattun fulas masu kyau ta sa farin kyalle mai dauke da falawoyi a jiki ta rufe ta yi saurin juyawa ta koma dakinta ta rufe sashenta ta shiga kicin dinta duk ta gyara kayan data bata, ta wanke komai ta goge ta mai da shi inda yake, sannan ta shige tolet dinta ta saki shaya a kanta ta fara wanka. Karfe biyu da rabi Haidar ya shigo gidan da carbi a hannunsa, "Yan matan kausar ya ga daya a bakin kofar falon tana gadin falon ta yi masa sannu da zuwa ya wuce. Ya shiga falon ya taba kofar jawahir a bame kamar yanda ta kwana. Ya girgiza kansa kawai, shi jin kansa ya hana shi kwankwasawa ya nufi bangaren kausar tana zaune a kan kujera 'yan matanta biyu suna gefenta daya tana yanka mata tufa a kan filet dayar kuma tana zuba mata abinci a daya filet din, wanda ya kasa banbancewa da kuskus ne ko burabusko. Yanda ya gan shi a dundunkule ya sha ruwa ya yi sharkaf. Ya zauna gefen ta 'yan matan suka yi saurin nikewa suka yi waje. Kausar ta dauki filet din abincinta za ta fara ci ta kalle shi ta ce, "Bismillah." Ya ce, "Wa! Ni? Allah ya sauwake na ci wannan abincin, ai sai na yi amai." Ta tabe baki ta ce, "Au kai fa ba ka cin abincin masu aiki ko? Ka sa kanka a wahala don yau na ga abin da za ka ci tun da na ga Sarauniyar taka fushi take yi bare ta zo ta girka maka. Wai ni kuwa yau ka yi break? Don ban ji motsinta ba bare na ji ko ta girka maka Ya ce, "Ke za a tambaya ba tare muka kwana ba, tsakanin ke da ita wa ya kamata ya yimin girki? Ta tabe baki, "Ka san ni ban tashi a cikin wahala ba don haka ba zan iya wani aikin komai ba. Da kake maganar da ni ka kwana ai tausaya maka na yi nake taya ka kwanciya don kada ka kwana kai kadai, me kake iya tabuka min? Ka riga ka zama nakasasshe, in ban da ka ishe ni da tabe-tabe ka tayar min da hankali babu biyan bukata." Ya daka mata tsawa tare da nuna ta da dan yatsa, ke saurara kada ki sake ki kawo min maganar banza a nan, da haka nake? Ko don lalura ta same ni za ki gaya min maganar banza, daure ki na yi ko cewa na yi dole ki zauna idan kin gaji ba dole, ba zan danne miki hakki ba ga hanya nan sai ki san inda dare ya yi miki. A ranta ta ce, "Ba inda zan je gwarzon namiji kamar ka ina zan iya barin ka, idan na yi sake ka subuce min ta yaya zan yi na mayar da kamar ka bare yanda na dandani zumarka ai sai dai na ga ba ka samu lafiya ba tukunna zan ki zama da kai. Ya gama banbamin fadansa ya fice yana tunanin tsananin hakurin jawahir da kawaicinta. Ya ji sallamar Hafsan faruk ya amsa mata cikin fara'a yau ina megidan naki na gan ki ke kadai? Wallahi yana office ka san bai taso ba, yanxu ma gidan yini zan je ya ce na fara biyo wa na ga jikin naka. Haidar ya ce, "Jiki Alhamdullahi." Ta zauna a falon suka gaisa ta ce, "Ina matan gidan ne? Ya ce, "Bari na kirawo miki su. Ya kwankwasa kofar jawahir ya ce, "Ki fito kin yi bakuwa, Hafsa ce ta zo. Ya juya ya nufi dakin kausar ya ce ki zo kun yi bakuwa, "Tace, "Wacece?" Ya ce, "In kin zo kya gani, "Ya juya ya fita. Jawahir ta bude falonta ta fito cikin dammamiyar riga body hook da jeans din wando da ya dame mata cinyoyi daga kasa kuma yake da fadi, kanta ba dankwali sai kananan kalba da ta tufka ta a bayanta ta kwanto guda biyar gaba. Ta yi kyau sai zuba kamshi take yi ta taho da dan gudunta ta fada jikin Hafsa tana dariya. Haidar kuwa ya zuba mata ido kallon ta yake yi yana hadiyar yawu, yarinyar nan kuwa ta san yanda take rikitar masa da hankali? Ta san yanda kirjin nan nata yake dauke masa hankali kuwa? Kausar ta shigo tana yatsina kujerar da Haidar yake kai ta nufa ta zauna masa kan cinya ya ce, "A'a ke me ye haka? Ta ce, Haba Darling kai ma ka san nan ne wajen zamana don ka riga ka sabar min. Ya ce, "Amma kina ganin bakuwa a wajen ko? Ko dan rashin kamun kai." Ya zame ta takaici da tsantsar kishi suka tokare zuciyar jawahir kamar ta yi kuka ta dan daure ta ce, "Hafsa tashi mu koma daki. Hafsa ta mike yayin da take gaisar da Kausar. Suka shiga dakin jawahir Hafsa ta ce, tab amma kina shan kallo, haka Kausar din take ba ta da kunya? Jawahir ta ce, "Ina ruwana da ita? Me ya dame ni da ita? Tun da ba zamanta nake yi ba. "Yanzu haka za ki zuba mata ido tana iskanci? In ni ce ai sai na nuna mata cewar ita karamar 'yar iska ce, bare yanda na ga hankalinsa da tunaninsa duk ya raja'a a kanki me ya sa ba za ki sakar masa jiki ku rinka farantawa juna rai ba.? Jawahir ta ce, "Kyale ni Hafsa ni na san halin da zuciyata take ciki a kan son Haidar, to kin san wani abu da yake damuna? Na tsani na bude ido na ga Kausar tana yi masa magana ko tana kallonsa bare ta hada jikinta da shi wallahi sai na ji kamar na je na shake ta ta mutu ko na huta. Hafsa ta ce, to bari na ba ki shawara wallahi yanzu yanda na fuskarki mijinki yana tsananin sonki mai zai hana ki fito masa da taki irin kissar kin san Allah nan gaba sai kin dinga tausaya masa don bin ki zai dinka yi kamar rakumi da akala saboda 'yar uwa ba dama ce fa ke, dole ne ki rikita Haidar, irin wannan cika haka komai ya ji, me zai hana hankalin Haidar tashi da gigicewa a kan ki.? Jawahir ta ce, "To ai ni ba ki sani ba kunyar hada jiki nake yi da shi sabo da sai na ga kamar zai ce min ba ni da kunya. Hafsa ta ce, "Tabdi jan zauna a barki a baya, au na gaya miki cikin dabara da hikima za ki rinka sakin jiki da shi kina yawan zama a duk inda yake ki rinka yawaita kwalliyar da za ta rikitar da shi kamar irin wannan sai kin zo kina ba ni labari da bakinki, "Hafsa ta yi zumbur ta mike bari na yi sauri na leka gidan wunin nan na koma gida kada Oga ya dawo daga office ba na nan. . S. Bomboy. WHATSAPP 0⃣8⃣0⃣3⃣8⃣4⃣9⃣1⃣3⃣9⃣3⃣ ♥♥♥SALON SO♥♥♥ ♥♥ PART 3⃣1⃣ ♥♥ . By Sulaiman Bomboy. . Jawahir ta yo mata rakiya Haidar yana falon tayi masa sallama Hafsa tana gaba jawahir tana biye da ita Hafsa ta fita daga falon jawahir za ta fita ke nan Haidar ya yi magana kasa kasa, "Kada ki fita harabar gidan nan da direba suka xo kada ya ganki. "Jawahir ta ja tunga suka karasa sallama da Hafsa tare da yi mata alkawarin zuwa in an kwana biyu, ita kuma ta tafi. Ta juyo daga rakiyarta har ta isa kofar dakinta ya kirawo ta. Jawahir ta tsaya kam, a wajen ba tare da ta juyo ba ta ce na'am, ya lankwasa murya ya a raunane ya ce, "Yanzu haka za ki bar ni na wuni da yunwa bayan kin san ba cikakkiyar lafiya ce da ni ba, ga shi lokacin shan maganina har yana kokarin wucewa, ta juyo a raunane cikin tausayawa ta ce, yanzu ba kaci abinci ba.? Ya dada langabewa to wa zai ba ni? Ke da kika san ciwona kike girka min yanzu gashi ba ki yi min ba. Ta ce, yaya na girka maka mana ta nufi tebir din ya biyo bayanta yanda ta ajiye haka yake ba wanda ya taba. "Ta bude komai ta jawo filet ta fito da tuwo malmala biyu ta cire su daga cikin ledar da ta zuba a filet din, ta zuba masa miyar a daya filet din ta tura masa gabansa kamar mai jira ya fara ci ta tsiyaya masa kunun aya, ya yi sanyi kuwa karara a gilas kof ta ajiye masa a gefe. Ta dan langabe kai ganin ya ture filet din tuwon ta ce, duk yunwar da kake ji dan wannan za ka ci? Ni jira nake fa ka cinye na kara maka wani. Ya ce, "Haba Babyna na cinye malmala daya da rabi ai dole na ji na koshi. Ta dan marairaice cikin shagwaba ta ce, to ci naman." Ta bude masa kamshinsa ya bige shi har na ji yawuna ya tsinke, ya kamo ta ya zaunar da ita a cinyarsa to zauna mu ci tare don na ga alamar ba ki ci komai ba. Ta langwabe a jikinsa ta ce, "Uhm Yaya na ci abinci fa a koshe nake." Ya ce, to gaya min me kika ci? "Yaya na sha yogourt da nama na kuma sha wannan. Ta nuna kunun ayar, da yake kofin. Ta dauko ta sa masa a bakinsa yaya kai ma dan sha ka ji akwai dadi. Ya kwankwada, "Uhm akwai dadi, dan karamin, ta noke tana yi masa dariya kasa-kasa ta ce, "Yaya ka ci naman tukunna kada ka cika cikinka da ruwan kunun aya. Ta yago naman ta sa masa abaki ya kama taunawa yana lumshe ido um carkwai wannan dadin haka kada ya tsinken kunne, "Ta kama shasshekar dariya tana langabewa a kirjinshi tana yago naman tana ba shi a baki. Duk abin nan da ake yi dauriya kawai yake yi don halin da jawahir ta tsunduma shi gaba daya ba shi da wani kuzari ta dada rikita shi da kaunarta da sha'awarta ta mamaye kowacce gaba ta jikinsa, ta mike yaya ka ji ana kiran sallar la'asar mu je mu yi sallah. Ya ce, to babyna na gode Allah ya saka da Alkhairi Ubangiji ya yi miki tukuici da gidan aljanna. Mu je na raka ki dakinki ko babyna ta langabe a gefensa yaya kada a tayar da sallah a masallaci ka je ka yi alwalar. Ya ce, "A'a yau a tolet dinki zan yi alwalar ta yi dariya to Yayana mu je. Yau dai a dakinta ya yi sallah don shi ya ja musu jam'i, ya dade yana kwararo musu addu'a sannan suka shafa. Yau dai wuni guda cikin farin ciki da annushuwa suka yi shi, gaba dayan su kokarin farantawa junansu rai suke yi bugun kofar da ake yi musu ne kamar za a balla ya sa Haidar saurin mikewa cikin fushi ya je ya bude, Kausar ce a tsaye tana girgiza kugu tana taunar cingam tare da yamutsar fuska, "Lafiya.? Abin da ya ce mata kenan. Cikin tsiwa ta ce, "To me za ka yi min ko ka manta cewar yanzu kai ba cikakken namiji ba ne ka zama miskini? Ai ni ba ka da amfani a wajena ita ma da ka ga tana rawar kafa don duk haka kuke ne ita ma ba me lafiyar ba ce don haka ta nakasta ka Ya daka mata tsawa, "Ke kausar ki shiga taitayinki ni ba sakaran namiji ba ne, ba ki isa ki wulakanta ni ba. Ita ma ta hau shi da ma sifa to ka sake ni mana haka kawai don zalinci ka ajiye ni ka san ba iya biya Min bukatata za ka yi ba, kana so da aurena ne na rinka bin maza kome kake nufi?" Ya ce, "To shi ke nan na ji ki yi hakuri zan yi shawara. Ta ce, "Ina son zuwa gidan kawata. Ya ce, "A dawo lafiya amma ki dawo da wuri tafi da direba can sai ya kai ki. Ta juya ba tare da ta ce masa komai ba. Kausar tana daukar mota ba ta wani tafi da direba ita kadai ta yi tafiyarta ta nufi gidan wata kawarta, ita ma 'yar Abuja ce aure ne ya kawo ta nan kano. Saddika ta tare ta da murna kausar amare yau nake zancen mun kwana biyu ba mu hadu ba, ina so in je gidanki ashe kina tafe. Ina angon naki ya barki kika taho ke kadai.? Kausar ta dauki lemon da ta ajiye mata ta kurba ta ajiye ta ce, kyale angon nan nawa ai ni na kusa barin gidansa. Saddika ta dafe kirji, "Haba kausar me ya yi zafi haka? Ki tuna irin wahalar da kika sha kafin ki samu Haidar ya amince ya aure ki, yanzu idan kika rabu da shi ta yaya za ki maye gurbin gayen yaro mai jini a jika da naira kamar Haidar?" Kausar ta tabe baki tare da yin tsaki ta ce, "Ai wadannan abubuwa da kika lissafa duk sun tashi a banza don yanzu ya zama solobiyon namiji ba abin da yake iya yi wa mace. Saddika ta ce cikin razana, "Ban fahimce ki ba, me kike nufi? Kausar ta ce, lokacin da na auri Haidar na same shi gwarzon namiji me cikakkiyar hallita wanda ya iya jiyar da mace dadi ko ta ina ban taba zaton zan iya rabuwa da Haidar ba don ta ko ina ya yi min Zamzam ga shi hadadden miji na nunawa sa'a, to dan bakin cikin matarsa ganin ba ta da lafiya komai bai taba gudanuwa a tsakaninsu ba shi ne ta yi min bakin ciki ta kwada masa abu a gabansa ta nakasta shi har kwanciya ya yi a asibiti amma likita ya ce ai ya riga ya nakasta. To yanzu ya dawo gida sai dai in mun kwanta waje daya da shi ya ruda min jiki da wasanni ba ya iya aikata komai wallahi ni na gaji gwanda ya sake ni na huta. Saddika ta ce, "Gaskiya yarinyar kamar ki da kuruciyarki da komai zaman hakuri bai kama ki ba, to amma ba kya tunanin wata rana zai samu lafiya ki zo kina takaici? Kausar ta ce, "Ke kuma kin ji ki da wata magana, likita fa ya ce min ba shi da wata ranar samun lafiya kina so na shiga yawon bin maza da aurena ne? Kinsan ko musulunci ya zama dole ya sake ni. Saddika ta ce, "Gaskiya ne da ki cilla kanki a halaka gwanda ku rabu kawai ki auri Bomboy ............ to amma ba kwanaki na ji kin ce kina da ciki ba."? "Ba ciki ba ne ashe batan wata na yi daga baya na ga al'adata ta zo. A nan ta yi sallar magariba suka ci abinci ta yi sallar insha sannan ta tafi gida. . S. Bomboy Whatssap 0⃣8⃣0⃣3⃣8⃣4⃣9⃣1⃣3⃣9⃣3⃣ ♥♥♥ SALON SO ♥♥♥ ♥♥♥ PART 32 ♥♥♥♥ . BY SULAIMAN BOMBOY. . Haidar da jawahir suna zaune a falo suna kallo jawahir ta kama hamma Haidar ya jawo ta jikinsa yana shafata ba dai bacci za ki yi ba ki bar ni.?" Ta daga kai ka san ni da baccin wuri bari na je daki na kwanta, "Ya langabe murya gaskiya ba za ki tafi ki bar ni tun yanzu ba." Ya rungume ta ya gyara mata kwanciya a jikinsa yana shafa kanta yi bacci a haka in na gama kallo na kai ki dakinki. Cikin mintina kadan bacci ya kwashe jawahir dadi ya cika zuciyar Haidar jin jawahir rungume a jikinsa taushin fatarta da kamshin jikinta shi suke dada sa shi nishadi. Kausar ta yi sallama ta shigo falon ba dan sanin muhimmancin sallama a addinin musulunci ba da bai amsa mata ba. Ya dako kai ya kalle ta, "Ina kika je sai yanzu da daddaren nan za ki dawo bayan na ce ki dawo da wuri.?" Ta kalle shi ta ja tsaki, "To ina ruwanka da dawowata da wuri ko ba da wuri ba? Kai ba wani cikakken namiji ba bare ka ce za ka yi kishina." Jawahir ta dan motsa ya sake rungume ta yana jijjigata kamar yarinyar goye. Kausar ta yi tsaki an dai fadi ba nauyi miskinin kawai kana luguiguita yarinya kai ba wani katabus za ka iya yi mata ba." Ta shige dakinta Haidar kuwa ya yi mata shiru ne gudun kada jawahir ta farka amma ya ji haushin maganar da ta yaba masa. Da ya ji kallon ma ya ginshe shi ba zai iya ci gaba da kallon ba, don tsananin dacin da zuciyarsa take yi Jawahir da tun shigowar Kausar ta farka ta ji duk abin da kausar ta gayawa Haidar ranta ya yi mugun baci, ba ta san sanda hawaye ya fara zubo mata ba. Haidar da ya yunkura zai mike da jawahir a kafadarsa sai ya kula hawayen da take yi hankalinsa ya sake tashi ya kira sunanta, "Jawahir lafiya?" Tayi saurin zamewa daga jikinsa ta durkusa kasa tana kuka ta fara rokonsa don Allah don Annabi yaya ka yi hakuri ka yafe min abin da na yi maka, ni na jawo maka matsalar da kake ciki wallahi tallahi ba da niyya na yi maka haka ba kan tsautsayi ne da kaddara, ina neman afuwarka da gafararka ko na samu sassauci a zuciyata." Ya mike tsaye ya kamo kafadunta ya dago ta ya rungume ta a jikinsa yana share mata hawayen, "Yi shiru babyna daina kuka ba so ki kuma irin wannan tunanin a zuciyarki, ki sani duk abin da Allah ya yi zai samu bawa daman tun fil'azal rubutacce ne, kuma babu wanda ya isa ya kankare shi ko ya goge shi. Don haka ki kaddara daman can Allah ya yi hakan za ta faru da ni, don haka ni ba na so na ji kina cewa ke ce sanadi kada ki kuma fada, ni na yarda da kaddara don haka ba na zarginki da komai, ki kwantar da hankalinki ba na son ganin ki cikin damuwa, kin ji ko. Ta daga kai alamar amsawa, "To mu je ki kwanta. Yana rugume da ita har dakinta, ya raka ta tolet ta yi borush ya riko ta sai da ya kwantar da ita a gadonta ya ja bargo ya rufe ta ya kunna mata A.C ya sumbace ta a kumatu ki yi bacci lafiya babyna. Ya juya ya fita ya nufi nasa dakin. Yana fita jawahir ta mike ta dauko tsaleliyar rigar baccinta ta saka ta shafe jikinta da humra. Ta dade feshe dakin da Air Freeshner nan da nan sanyin A.C da daddadan kamshi suka shiga tashi. Ta matsa mouth freeshner a bakinta nan da nan sanyayyen kamshi ya rinka fita ta haye gadonta ta yi lumtsim da ita. Haidar ya shigo wanka ya fito ya shafe jikinsa da turare ya hau gado dan kwanciya amma ina baccin ya gagara sai juyi yake yi yana tunano lallausan jikin jawahir da taushinsa, ya san ina bacci zai dauke shi, ya sa kayan baccinsa ya fito ya rufe dakinsa ya nufi dakin jawahir. Ya sa safayar mukullinsa ya bude dakin ya shiga ya mayar ya rufe. Ya shiga cikin dakin nata wanda sanyin A.C ya gama ratsa shi, ga man nan na turarenta mai dadin kamshi yana tashi. Ya kunna fitila ya yaye bargon da ta rufa ya kalle ta cikin tsaleliyar rigar baccinta wadda ta kara fito mata da sigar kyanta, baccinta take yi hankali kwance. ♥♥♥ SALON SO ♥♥♥ ♥♥♥ PART 33 ♥♥♥ . BY SULAIMAN BOMBOY. . Ya kashe fitilar ya hau gadon ya shiga cikin bargon ya sa hannu ya shafo ta. Cikin razana ta farka a firgice ta yi zumbur ta mike tsorace tana wayyo Allah na Yaya na shiga uku, wayyo Allah yaya na ka zo ka cece ni." Ya mike shi ma ya riko ta, ta dada firgicewa tare da sa kuka, "Wayyo na shiga uku yaya ka zo ka cece ni." Ya ce, "Jawahir meye haka? Ni ne fa Yayanki Haidar ba ki gane ni ba ne? Ya kunna fitila ta daga kai ta kalle shi ta mayar dakanta kan kirjinsa ta kwantar tana ajiyar zuciya. Ya sa hannu ya zagaye ta ya kashe fitilar ya yi gadon da ita. Ya kwanta tana manne a jikinsa, jikinta sai bari yake yi na tsoratar da ta yi. Zuciyar Haidar fes yau ga shi manne da jawahir dinsa, abar sonsa shi kuwa ya taba jin jiki me taushi da santsi kamar na jawahir dinsa? Shi dai bai gushe ba yana sambatu da jin dadin tattausar jiki har bacci ya kwashe shi. Da asuba ya riga ta tashi sai da ya dauko alwala sannan ya tashe ta ta tafi yo alwala kafin ta dawo ya tayar da raka'atainil fajri ita ma ta tayar suna idarwa suka tayar da sallar asuba Haidar ya ja musu limanci. Suna idarwa suka ja carbi suka yi ta yin addu'a har suka shafa ya bude musu kur'ani suka biya tare suka sake yin addu'a suka shafa. Ta durkusa gabansa yaya ina kwana. Ya amsa cikin murmushin jin dadi kin kwana lafiya yaya tsoro? Ta yi murmushi ta mike ya ce, "Ina za ki? Sai da ta rissana sannan ta ce, "Kicin za ni. Ya ce "A'a taho kwanciya za mu yi suka koma gado suka kwanta. Bacci ya dade da kwashe su wani gigitaccen bugu ne ya farkar da su a wahalce Haidar ya zare jikinsa daga na jawahir ya mike ya nufi kofar ya bude. Kausar ce ta cukuikuye masa wuyan riga tana cewa, "Kai wallahi sai ka sake ni takardarta za ka ba ni ba zan iya zama da miskini ba. Ya wankawa fuskarta mari ya ce, "Ni kika shakarwa wuyan riga, dan iska za ki mayar da ni? An ki a sake ki din ki je ki gayawa duk wanda za ki gayawa. Ta dafe kunci ni ka mara to wallahi sai ka gane kurenka. Ta juya ta yi dakinta ta dauko mayafi ta yi waje ta hau mota ta tuka kanta ta fice daga gidan. Kotu ta nufa ta shigar da kara. Haidar yana gida sun gama shirinsu sun ci kwalliya kamar masu xuwa fati, sun gama karyawa ke nan yaron gidansa ya yi sallama a kofar falon aka amsa masa ba tare da ya shiga ba ya ce Yallabai ana sallama da kai a waje. Ya ce, "Okey ga ni nan fitowa. Ya mike ya fita Da mamakinsa suka gaisa da bako ba tare da ya san shi ba. Bako ya mika masa zungureriyar takarda, "Ni yaron alkali ne ga shi wannan sammaci ne daga kotu matarka tana kararka. Haidar ya rinka juya takarda a hannunsa cikin mamaki ya ce, "Okey je ka na gani. Yaron alkali ya juya ya tafi, Haidar ya shiga gida Ya cewa jawahir zai je gida yanzu Abbansa yana son ganinsa. Ta yi masa kyakkyawar addu'a tare da fatan Allah ya dawo da shi lafiya." A hankali ya rinka juya motar yana mamakin hali irin na kausar. Yana isa gida ya samu Abbansa a falo da Anti suka gaisa sai ya mikawa Abbansa takardar da aka kawo masa ya ware takardar ya karanta. Abba ya hangame baki tare da yin salati. Cikin yaya? Me ya hada ku? Haidar ya kwashe labarin komai ya gaya masa. Abba ya kama salati amma wannan yarinya ta ci mana mutunci. Anti ta ce ka sake ta kawai ba sai an je gaban kotu ta tsinka mu ba. Nan take Haidar ya rubuta mata takardar saki daya Anti ta karba ta bawa me aikinta tace ta yi sauri ta je direba ya kai ta gidan Saddika kawar Kausar su kaiwa Kausar din. Kausar kuwa tana ganin takarda ta cika da farin ciki inda a nan take ta yi wa alkalin waya ta ce ta janye shari'ar ta yi sauri ta koma gidan Haidar daman ta sa 'yan matanta sun hada mata kayanta na sawa da duk wani abu na amfaninta na kwalliya suka judo mata akwatunanta suka loda su a but direba ya je su zuwa Airport suka yanki tikiti suka nufi Abuja. Abbab Haidar ya dube shi ya ce, "Bana so ka sa damuwa a ranka bare ka zo abin yana damunka daman na gama shirya muku tafiya xuwa kasar waje Kai da jawahir za ku je asibitin Cairo sabo da haka ku je ku fara shiri nan da sati daya za ku tafi. "To Abba mun gode Allah ya saka da alheri Ubangiji ya kara budi. Haidar ya koma gida yake gayawa jawahir abin da ya faru duk da jawahir ba ta son zaman Kausar a gidan amma ba ta ji dadin sakin da Haidar ya yi mata ba. Ba su da wani lokaci sai na shiri da ziyartar 'yan uwa suna yi musu sallama. Ranar da suka je Abuja gidan Ankul Anti Maryam ta ce ya dai 'yata in ce ko dai har yanzu kina shan abubuwan da na gaya miki? "Ai Anti tun ranar da na bar gidan nan ban yi fashin shan kayayyakin nan ba, don wasu abubuwan ma idan na hada har da Yayan muke sha ba tare da ya san ko meye ba. "Yauwa diyata na sara miki yanzu na san kin tsumu kin cika da ni'ima sosai karyar Haidar ya dandana ki ya kuma kusantar wata matar. "Allah Auntyna, "Suka tafa. Aunty maryam ta kwaso mata wasu hadin da ta kuma yi tare da wani turare na gama da ake yi kafin saduwa da miji, tsaraba dai sosai ta hada mata don tafiya Cairo. Sun je gidan Inna gidan Yagwalgwal, gidan Faruk, gidansu Bilkisu, gidan Abba, gidan Dady, duk gidan dangi da 'yan uwa babu inda ba su ziyarta ba. Sha biyu na dare jirginsu ya tashi xuwa kasar Egypt wato inda za su sauka a birnin Cairo inda asibitin da za a duba Haidar yake. Ranar da suka dira gajiya ba ta bar su ba ramuwar bacci suka yi sai washegari suka isa asibitin. Aka saka Haidar a computer cikin lokaci kankani suka gano matsalar ba tare da bata lokaci ba suka yi masa aiki suka kwantar da shi a asibitin tsawon sati daya saboda magungunan da yake sha. Cikin ikon Allah Haidar ya ware ya samu sauki kamar ba shi ba. Asibitin sun sallame shi sun dawo Hotel din da suka sauka. Yana kwance a kan kafet jawahir tana masa tausa sannu a hankali yana wash! Wash!! Tare da lumshe ido. Yau duk ya wani shagwabe mata ya narke mata ta hana ta sukuni daga ya ce, nan yana cuwo sai ya ce can. Sai bin sa take da lallama cikin tausayawa da kyar ta samu ya yi bacci ta shiga tolet ta yi wanka ta fito ta gyara jikinta da hadadden mayuka masu kamshi tare da turarukan da ta mulke jikinta kowacce gaba ta jikinta kamshi take fitarwa. Ta saka 'yar bingilar rigar bacci iya cinya me hannun shimi ta dada feshe dakin da Air freeshner. Dakin ya dau sanyi da daddadan kamshi ta haye gado ta shiga bargo ba ta jima ba bacci ya yi awon gaba da ita. Haidar da idonsa yake a kanne yana kallonta ya mike shi ma ya shiga tolet ya watsa ruwa ya fito ya gama shirinsa ya hade jikinsa da kamshin turare, ya kashe fitila ya hau gadon ya kunna dim night dakin ya yi shiru ba ka jin motsin komai sai karar A.C Haidar ya manne ta a kirjinsa ya matse ta gam, ya tura harshensa cikin bakinta ya rinka tsotsa yana wani salo na daban. Da ya gangaro zuwa kirjinta yayin da ya zare karamar rigar da take jikinta. Bayyanar na shanunta a waje shi ya kara gigitar da shi jikinsa ya hau bari da rawa ya gigice ya dimauce har ya manta a wacce duniyar yake. "KASH MASU KARATU KU YI MIN HAKURI MU HADU A KASHI NA UKU DON JIN HANYOYIN DA JAWAHIR TAKE BI DON SIYE ZUCIYAR HAIDAR YA ZAMO BA SHI DA TUNANIN WATA DIYA MACE SAI ITA. SANNAN KU JI KAUSAR ZA TA AURI BOMBOY DIN NE KO KUMA DAI............ KU BIYO NI A KASHI NA UKU AMMA SAI NAGA COMMENT DA YAWA IDAN DAI DA GASKE KUNA SUN CIGABAN. . SANNAN MURA TA RIKE NI WATA/WANI TAYI/YAYI VOLUNTEER TA/YA SAYO MIN TOM-TOM IDAN KUMA NAJI SHIRU............. HMMMMMM . SAI MUN HADE. (((((SALON SO))))) (((((PART 34)))))) : By sulaiman 8omboy. . Tunda kun hana ni Tom Tom dina shikenan, amma fa........ Ko da yake ba sai na fada ba. . Jikinta ya rinka rawa da karkarwa kamar mazari. Ta kasa wani katabus sai kuka data ke yi tana yi masa magiyar daya hakura ya kyale ta. Haidar kuwa kusan ma iya cewa hankalinsa baya jikinsa saboda samvatu da ya rinka yi yana surutai. Hankalin jawahir ya tashi, ta rinka dukan Haidar tana girgiza shi yayin da ta tsala wata kara shi kenan Haidar ya cika aiki. Sai da Haidar ya gama samun nutsuwa hankalinsa ya dawo jikinsa sannan ya kula da halin da jawahir take ciki sai nishi take yi sama-sama fuskarta da fulon da ta ke kai sun jike da gumi da hawaye. Inna lillahi wa'inna ilaihir raji'un, ya dago ta yaga ta koma ta langabe a hankali ya ajiye ta a gadon ya nufi tolet ya cika baho da ruwan zafi ya zuba datol yaje ya dauko ta ya sakata a ruwan zafin ya rinka buda mata kafafuwanta ruwan zafin yana ratsa ta. Ita kuwa Jawahir sai 'yar kara take yi irin ta galabaitar nan da wahala. Haidar kamar zai yi kuka saboda tsananin tausayinta. Sau uku yana canza mata ruwan ya karanta mata niyyar wanka ta fada a zuciyarta, ya yi mata wankan tsarki shima ya yi yana dota a tawul ya kawo ta dakin ya zira mata doguwar riga shima yasa jallabiya. Ya dauki waya ya bugawa likitan hotal din cikin lokacin kankani ya zo ya duba jawahir ya yi mata allura ya ba wa Haidar magungunan da zai bata tasha. Likita ya yi musu sallama ya fita Haidar ya tsiyaye mata madarar kwali a kofi tana manne a kirjinsa duk ta wani langabe don bata da kuzarin komai sai tsananin kasala da ciwon jiki ga radadi da yake damunta. Ya dago kanta ya sa mata kofin a bakinta ta langabe cikin shagwaba ta ce ni bazan iya sha ba, yi hakuri bebi na dan sha kurbi kadan kin ji kinga magani zaki sha don jikinki ya wartsake Ta kurba ta hadiye da kyar, ta kau da kai, "Yi hakuri dan kara kadan kinji bebi na. Da lallashi da lallama ta dan sha da yawa ya bata maganin da ruwa ta sha ya dauke ta suka koma daki lokacin karfe biyu na dare, ya kwanta a gadon ya dorata a kirjinsa ya rungume ta tana ta faman raki wayyo yayana bayana kuguna kaina yaya ko'ina ciwo yake yi min "Sannu bebi na Allah ya yi miki albarka hakika kin cika 'yar halak da ki ka kawo min budurcinki lafiya. Allah ya yi miki albarka Allah ya saka miki da alheri. Ubangiji ya bamu zuri'a ta gari." Ya rinka shafa bayanta yana yi mata tausa kadan- kadan, yana mammatsa mata jikinta bacci ya dauketa. Haidar ya rungume ta ya kankame kamar wani zai kwace masa ita, amma maganar bacci babu ita don tsananin dadi da zumudi ya hana shi gyangyadawa. Mamaki ne ya cika zuciyar Haidar yanda ya ji dandanon zumar jawahir yanzu jawahir din da ya raina ce Allah ya wadata ta da ni'ima haka? Lallai dan hakin da ka raina shi yake tsone maka idonka. Yau dai kam ga shi jawahir ta tsone masa idon, lallai Allah yana sonsa da ya dawo masa da jawahir bayan subuce masa da tayi a baya, Allah ya taimake shi bai yi wautar sakin ta ba. Ai dole ne ya tashi ya yi nafila don nuna godiyarsa ga ubangiji a bisa wannan baiwa da Ubangijin ya yi masa, na mallaka masa gwarzuwar mata mai cikar halitta da wadatacciyar ni'ima. A hankali ya zare jawahir daga jikinsa ya kara mata fulo don kar ta farka ya nufi toilet ya dauro kyakkyawar alwala ya zo ya fara nafula raka'a goma sha biyu ya yi wa Annabi salati kafa dubu, ya daga hannuwansa sama yai ta kwaraea addu'a, yana yiwa Allah kirari da yaba su zaman lafiya da zuri'a me albarka shi da matarsa jawahir. Sai da aka yi kiran assalatu ya tashi jawahir suka yi sallar asuba, suka koma suka kwanta. Sha daya na safe Haidar ya farka ya zare jikinsa a hankali ya nufi toilet ya fara wanka Jawahir ta bude idonta ta tashi ta daddogara a hankali ta fito daga wannan dakin ta shiga dayan itama ta fada toilet Da yake falo ne da dakuna biyu a cikin falon wanda suka kama. Jawahir ta fito daga wanka ta tsane jikinta da tawul, ta shafe jikinta da hadaddun mayukanta masu kamshi da sa taushin fata hade da santsin jiki. Ta rinka mulke gabobinta da hadaddun turaruka na jiki masu dadin kamshi. Ta tsala kwalliyar fuskarta yanda yaka mata fuskar sai sheki take yi ta yi sumul sumul abun sha awa. Ta saka wani tsadaddan farin yadi sol mai dishi- dishin gwal din a jiki 'yar karamar riga ce fitet me dan guntun hannu rigar ta yi mata cif a jikinta. Sai siket din da ya yi mata tsantsan duk wata sura ta jikinta ta bayyana ba ma kamar kirjinta da yake cike da dukiyar fulani a tsattsaye suna barazanar tsokane idon me kallon su. Ta sha adon gwal yari da sarka manya ga awarwaro da zobuna tuni ta dauki kyalli tana sheki Tasa farin takalmi tana fesa turare ta ji dhigowar Haidar ta yi saurin boyewa a cikin labulaye: Haidar shima ya shirya cikin wani lafiyayyen boyel fari kal me laushi sai fitinan nan kamshi ne yake tashi a jikinsa kamar ya yi barin turare. Ya shigo dakin ya kama wara ido don ganin in da zai hango tauraruwarsa ga shi dai duk kamshinta ya cika dakin. Kafarta ya hango ta kasan labulan ya nufo wajen ya janye labulan tasa hannu rufe fuskarta. Ya tsane yana karo mata kallo cikin zafaffiyar kaunarta da matsananciyar sha'awarta. Ya jawo ta jikinsa ya manne ta a kirjinsa yayin da kaunar ta take dada ratsa zuciyarsa. Cak ya dauke ta yayo falo da ita suka zube akan kafet don karyawa, tana makale a jikinsa shi ji yake ina ma zai iya tsaga jikinsa ya tura ta ciki da sai ya fi masa sauki da yanda kaunarta take addabarsa a zuciyarsa. A baki ya rinka ba ta break din cikin lallashi da lallama don shi da da hali ma tauna mata zai rinka yi don ta samu saukin hadiya. Sai da ya tabbatar ta koshi sannan ya rabu da ita shima ya ci ya yi kat. Ya shiga wasanni da sassan jikinta in da ita kuma ta takure waje daya ta ki bude fuskarta. Ya dauke ta cak ya yi gado da ita yana cewa "To bari mu maimaita abun jiya tun da kin fi so ko?' Cikin marairaitar murya ta ce, "Wayyo Yaya don Allah ka kyale ni bana so yayin da ta kwabe fuska take kokarin yin kuka. Ya rungume ta "Sorry bebi na kada ki yi kuka da gangan nake yi miki. Rufe idonki, "Ta rufe yayin da ya saka mata 'yar batta guda biyu manya a hannun nata duk ya bude su. Ya ce ta bude idonta tana budewa taga custume yari da sarka da zobe manya tafka tafka kirar dubai sarkar mai harafin H/J, sai daya battar kuma manyan warwaraye ne guda hudu gaba daya Daimond kudinsu a kalla zasu yi dubu dari biyar da doriya. Bude baki tare da kwalalo ido ta ce "Yaya wannan fa? "Kyauta ce nayi miki don farin cikin yanda na riske ki. Ta kankame shi cikin murna yayin da ta lalubi bakinsa ta yi masa kyakkyawar sumbata, ta ce "Yaya na gode Allah ya saka maka alheri Ubangiji ya raba ka da sharrin makiya." Ya ce "Amin babyna, na gode da addu'arki Allah yasa mun samu rabon bebi a daren jiya ko kuma in an jima mu samu." Cikin shagwaba ta bigi kirjinsa "Um, um ni dai yaya ba za'a kuma ba da ciwo." "To shi kenan kada ki yi min kuka ma arahar hawaye." "Yaya ya aka yi ka samu masu harafin sunanmu.?" Ya ce, "Ai tun ranar da muka fara ziyartar asibitin kafin ayi min aikin nan naje gurin da suke kerawar nasa su kera min don zuwan wannan rana. "Kai Yaya amma kuwa na gode Allah ya saka da alheri Ya dora hannunsa akan bakinta ya ce "Shit bana son yawan godiyar nan kuma ki cire wannan Yayan da kike gaya min bana so. Cikin kashe murya da kissa ta ce, "To me zan dinga ce maka? "Ke za ki zabo da kanki ki rada min. Ya kawo kunnansa daidai bakinta "To gaya min naji". Cikin kasa kasa da murya ta ce, "My love yayi maka?" Ya rungume ta yana ihun murna yayi ya yi kwarai babyna kin iya zaben suna. Ta rufe idonta tana dariya. Ta kama lumshe ido irin na me jin bacci. Ya ce, "Bacci babyna.?" Ta daga kai kwantar da ita a kan gadon to kwanta na yi miki tausa. A hankali ya rinka yi mata tausar yana dan matsa mata jikinta. Sannu a hankali bacci yayi awon gaba da ita ya zuba mata ido yana kallon tsabagen kyau da Allah ya bata. Ga komai nata cif-cif ba abin da ya fi ba shi mamaki yanda ya jita tamtsan cike da ni'ima ga kirjinta cike da dukiyar fulani abun da yafi sha'awa da daukar hankalinsa a jikinta. Shima kwanciyar ya yi ya manne a jikinta ya kankame ta har sai da ta yi 'yar kara ta ce my love sannan ya sassauta mata rikon. Sai bayan Azahar suka tashi suka sake sabon wanka tare da yin alwala ya ja musu limanci suka yi sallar Azahar. Daga nan suka sake sabon shiri shigar kananan kaya suka yi ke in kin gansu sai ki zata Indiyawa ne. Suka ci kayataccen abinci me rai da lafiya, Haidar ya jawo ta jikinsa babyna mu dan fita mu zaga gari ko? In nuna miki wajajen ban sha awa da na kayatarwa. Ta noke a jikinsa tare da cewa "my love ka bari sai gobe jikina har yanxu yana yi min ciwo." "Ciwo babyna! Kada fa ya kawo mana matsala in an jima fa.? Ta bigi kirjinsa cikin wasa tana harararsa, "Allah Allah my love ka bari zan yi maka kuka. To na bari na bari babyna, tana langabe a jikinsa sai shagwaba take yi masa du ta wani narke masa sai zuba masa sangarta. Shi kuwa gogan ya rikice duk ta burkita masa tunani da sha'awarta sai riritata yake yi yana lallaminta, tare da taba wasanni a jikinsa nata ko zai samu 'yar nutsuwa kwana hudu yana jirarta ba tare da ya kuma neman yin wani abu da ita ba, sai yai ta faman riritata yana sangartata yayin da take zuba masa shagwaba son ranta shi kuwa yai ta biye mata don bata da masaukin da ya wuce jikinsa, ko yaushe tana manne a jikinsa yanayi mata tausa ko wasanninsu na ma'aurata. Aha har yanxun xa'a bani ko kuwa sai na kuuma? Idan kuuma ba'a bani ba............ hmmmmmmmmm ((((( SALON SO)))) ((((((PART 35))))) : By Sulaiman Bomboy. . Kamar yau ta sha wankanta ta kayata fuskarta da dogon wandon ta shima pick colour me baza daga kasa sai bakin gashinta da ya kwanta a bayanta yana ta zuba kamshi da sheki. Ta yi tsananin kyau irin kyan da baya misaltuwa, ta zira siririyar sarkarta da yari da abun hannu duk na gwal, jikinta sai ni:imtaccen kamshi ne yake tashi kamar anyi barin turare a jikinta. Ta fito falon in da yake zaune yana kallon wakoki cikin tashar turawa. Ta zo ta zauna a cinyarsa ta sakalo wuyansa da hannuwanta ta yi kasa-kasa da muryarta yayin da take kashe masa ido daya ta ce "My love ince ko dai baka yi fushi ba na barka kai kadai? Ya rungume ta tsantsan a jikinsa "Babyna ina sonki da yawa kina sani farin ciki koda yaushe duk sanda na kalle ki ina kasancewa cikin nishadi da annushuwa, bebi na ki yi wani abu akan yawan kaunarki da nake na zarme da yawa." Ta hada fuskarta da tasa ta tallafa kansa ta zira harshenta a bakinsa ta shiga juyawa cikin wani irin yanayi na SALON SO." Ta fa gigita shi ya ji wani abu yana tsikarar zuciyarsa ya rikide mata ya shiga sumbatarta ba kakkautawa, ya zira hannunshi cikin rigarta yana wasa da yana mata wani shu'umin kallo mai burkita kwakwalwa cikin kunnanta ya rinka rada mata kiyi hakuri bebi na ki bani hadin kai na nuna miki irin tsantsar kaunar da nake yi miki, ki taimake ni bebi na muraya daren yau don samun ladan sunnah". Ta yi zumbur ta mike cikin yanayi na tsoro da jin kalamansa, shima ya mike ya riko hannunta ta marairaice fuska tana son yin kuka, "Ka tausaya min Yaya wallahi akwai ciwo." Ya rungume ta ya dora kanta kan kafar shi yana rarrashinta "Ki yi hakuri babyna ba zaki ji ciwo ba, wancan ma don na farko ne shi yasa ki ka wahala amma ba zaki sake jin ciwo ba, ki taimaka min ki bani hadin kai gudun kada ciwon mara ya dame ni kin ji bebi na kin amince? Ta daga kai cikin yanayi na rauni da damuwa. Ta bashi tausayi ya san bata so don ta wahala ranar nan, ga shi, shi kuma tun da ya dandani yanda take ba zai iya hakure mata ya sa mata ido kamar da daya zuba wauta ba. Amma insha Allahu zai bi ta a sannu don ta samu sassauci. Haka ya rinka lallabata yana bata damammiyar madara da gasasshen nama mai ruwa ruwa. Duk wani abu da zasu gudanar sun gudanar, wanke baki shafa turaren gabobi, matsa mounth freshner a baki fesa Air freshner, a kowacce kusurwa ta dakin inda sanyin dadin ya rinka fita sabo da sanyin AC da dadadan kamshi da ya hadu ya dauke ta cak yayi gado da ita ya rinka yi mata wasanni ya taba can, ya tsotsi can ya murza nan cikin dan lokaci kankani ya kashe mata jikinta da salon kaunarshi. Tana jin shi yana zame mata kayan jikinta amma bata da wani katabus bare ta yi yunkurin hanawa, sannu a hankali ya rinka binta har ya cimma burinsa. Ga mamakinta sai ta ji bata ji ciwo da zafi kamar na ranar nan ba. Bayan hankalinsa ya dawo jikinsa ya rinka rarrashinta da lallaminta yana yu mata tausa har bacci me nauyi ya dauke ta. Yayin da shima ya manneta a kirjinsa hannunsa yana kan nononta yana wasa da shi har bacci ya yi awon gaba da shi. Karfe bakwai ta farka ta ji ta manne a kirjin Haidar ta rasa yanda zata yi don ba taso ta yi motsi don kada ta yi motsi don kada ya farka saboda yau wata irin kunyarsa take ji tare da wata irin zazzafar kaunarsa da take ratsa dukkan gabobin jikinta. Ya bude idonsa ya rinka dubata cikin sha awa yayin da tasa hannuwanta biyu ta rufe fuskarta tana murmushi da ita zata shi a jikinsa suka shiga bandaki tare suka gudanar da wankan lokaci daya suka dauro alwala suka fito suka gudanar da sallar asuba a makare. Ya matsa kusa da ita ya zare hijabin da ta yi sallar ya kwanto da ita kan cinyarsa ya kura wa kirjinta ido. Yana kallon manyan mamanta da suke cike jajir da su a tsattsaye basu da niyar rankwafawa kamar wanda aka da sa su ko da yake dashin Allah ne Jawahir tasa hannunta ta rufe masa idonsa don ganin irin shaidancin kallon da yake yi mata ta san ba za su waye lafiya ba. Ya dan ciji hannun nata ta janye cikin sauri ya tsirawa fuskarta ido yana kallon kyakkyawar fuskarta. Ta lumshe idanuwanta ya zura harshensa yana lasar girarta zuwa kumatunta Ta sakala hannuwanta a bayansa ta tallabe shi sosai ya zira harshensa cikin bakinta suka ci gaba da farantawa juna rai. Bacci ya kuma kwashe su sai shabiyu suka tarka lokacin suka tsala wanka suka shirya Haidar ya shirya cikin jins da damammiyar T-shirt me gajeran hannu jikinta layi layi ne na fari da ja, ya yi kyau sai kamshi yake kwararawa. Ya dawo falo ta kwanta a doguwar kujera yayin da ya kunna T.V yana kallon tashoshin Turawa yana jiran jawahir ta fito suyi break. Jawahir ta gama shirinta cikin damamman guntun wando da 'yar bingilar riga iya cibiya, gashinta ya sha gyaran sai sheki yake zubawa da kamshi jikinta kuwa sai fitar da nau'ikan kamshi suke yi masu narkar da zuciya. Ta ta ko a hankali kamar bata son taka kasar ta fito falon tun kafin ta karaso falon Haidar ya kafa mata ido, kaunarta tana kara ratsa shi kamar ya hadiye ta don so. Ta tako a hankali har zuwa kan kujerar da yake ta kwanta dai dai a cinyarsa, ya yi wata irin wawar a jiyar zuciya, ya kuma rungume ta babyna zo muje na baki break kada yunwa a illata min ke, ta langabe a jikinsa tare da kiransa "My love ya ce "Na'am bebyna ya aka yi? "Wallahi my love gida nake tunani yaushe za mu koma mu ga iyayenmu da 'yan uwanmu? Ya kara rungumarta "Haba Bebyna muna tare da ke ki ke son koma wa gida ki yi min adalci mana ya kike so nayi da dinbin kaunarki na ga baki damu dani ba." Ta yi saurin sa tattausan hannunta ta rufe masa baki "Yi hakuri my love ba nufina ba kenan wallahi ina sonka ina kaunarka zuciyata tana son kasancewa tare da kai koda yaushe. Ya yi mata kyakkyawar runguma yana sumbatarta da haka suka je suka yi kataccen break. Ya dauko abayarta ya sa mata ya rufe mata kanta da karamar hijabi fari mai kyau yaja hannunta suka fice yawon zaga gari. Hakika ta sha kallo ta yaba da tsarin kasar London gari ne me kyau da ban sha awa. Ita dai ba don tunanin iyayenta da 'yan uwanta ba, da ta roki Haidar su dawo kasar nan da zama sai dai ba za ta iya ba saboda kulafucin iyaye da 'yan uwanta. Sun zaga sosai daga nan suka dire a wani hadadden gidan abinci girke girkensu sun kayatar da jawahir ta ji dadin abincin sosai har ta rinka santi. Sai yamma likis sannan suka koma masaukinsu. Washe gari ma wajen sga biyu suka fita, ya rinka zagayawa da ita suka dire a wasu kamfani na kera akwatuna ya zabo mata set biyu masu kyau sabon dizayin don a lokacin ma ba su zo nan ba. Da masu ruwan zuma da masu ruwan toka. Daga nan suka wuce wani tafkeken shago na saida gwala gwalai, tare suka rinka zagayawa, duk in da ya hango me kyau in dai ta bashi sha'awa ba ruwansa da tsadarta sai ya dauko mata sarkar kafa me kyau ya kara a kafar jawahir tuni ya ga sun kara haskakat kafar tata Ya kuma dakko sarkar hannu itama ya kara mata subuhanallah tuni yaga kyakkyawar matar tasa ta sake fitowa sosai Abin ya ba wa jawahir mamaki, yanda ta ji an buga kudin mai yawa taga ya biya duk tsadarsu bata re da ya damu ba. Ta matso dab da shi ta kwantar da kanta akan kafadarsa ya sa hannu biyu ya rungmeta "My love don Allah ka daina yawan kashe min kudi don hidimar da kake yi min ta yi yawa. Ya dada rungume ta yana dan bubbuga bayanta kada ki damu bebyna komai na mallaka a duniyar nan naki ne ki daina damun kanki don na kashe miki 'yan kalilan din kudi." "To Yayana na gode Allah saka da alheri Ubangiji ya kara budi. "Yauwa Bebyna, amin" Ta rada masa a kunnensa "My love" mu koma gida abincin jiya." Cikin dariya ya kama bakinta wannan bakin ya iya kwadayi ko, ta manne kanta a kirjinsa tana murmushi suka wuce gidan abincin. "Yan kwana biyun nan jawahir tana fama da yawan kasala da lalaci ga yawan bacci, yanxu basu fi ya dadewa hira ba sai jawahir ta kama bacci. ❤❤❤SALON SO❤❤❤ ❤❤❤ PART 36 ❤❤❤ . By Sulaiman Bomboy. . Abin da Haidar yake dauka yawan gajiyar da ita da yake yi ne shi yake yawan sa mata kasala. Yau ma tare suka shiga toilet wanka suka yi suka cuda junansu cikin farin ciki tare da wasanninsu na ma'aurata. Ya kinkimota ya fito da ita ta zille daga cikin sa ta koma daya dakin don ta shirya. Haidar ya gama shirin cikin wando iya gwiwa wato tree gwata da riga marar hannu me kyau yana ta kyalli don shima fatarsa ta kara gogewa. Kowa ya kalli shi yasan fatarsa ta kara goge da hutu da jin dadi irin na masu da shi. Jawahir ta gama shirinta wani mini siket iya cinya da ya matse mata cinyoyi sai dai yana da tsaga gaba da baya. Rigarta iya kirjinta ta tsaya cibiyarta a waje ta ke fuskarta ta kara haske da kyau da kuruciya yarintarta ta kara fitowa fili. Jikinta sai fitinannen kamshi ne yake tashi me ta da sha awa. Ta dawo dakin da ta bar shi saboda zazzabi da ta ke ji ga ta shin zuciya, yana tsaye yana fesa turare ta zo ta kwanta a bayansa tare da zagaye shi da hannuwanta ya kamo ta ya zagayo da ita gabansa tare da cewa "Bebina lafiya me yake faruwa ne da ke, jikinki duk ya canja ga yawan lalaci da bacci.? Ya dauke ta suka koma kan kujera suka zauna yana lallatse jikinta don ganin ta kamaimai me yake damunta, duk ta narke a jikinsa ta langabe tana ta zuba masa shagwaba tare da marairaita. "Bebina muje asibiti a duba min ke don na san me yake damunki. Cikin ma rairaita ta ce "My love ni bana so muje asibiti don kada suyi min allura idan na sha fanadol ma zan samu sauki" Ya ce "Haba bebyna ya za ayi na barki haka kin ji jikinki kuwa yanda ya dau zafi ya kama lallatsa wayar likitan Hotel din ta rike hunnansa kamar za tayi kuka. Don Allah "My love kada ka kirawo shi wallahi na sha magani zan ji garau. Ya ce ke dai kin fiye tsoron Allura." Ya hada mata break yana bata a hankali tana kau da kai alamar ba ta so don bata jin dadinsa ya rinka lallaba ta yana ririta ta har ya samu ta dan ci. Ya bata magani ta sha ta kwanta a jikinsa tana dan yi mata tausa tare da mammatsa mata jikinta. Bacci ya kuma dauke ta ya gyara mata kwanciya a jikinsa lokacin da ta tashi jikin nata da sauki daga nan London suka wuce kasar America jawahir tayi mamakin yanda taga Amerika ashe itama haka take da kyau gaskiya kasar ta bata sha awa. Nan ma Haidar ya bude bakin aljihu yai ta narka mata kudi kamar vai san zafin nema ba. Watan su daya a Amerika suka dire kasar Saudiya jawahir tayi kyau har taga ji da kyau ta kara haske da kuruciya, duk wanda ya kalle ta zai gano yaron ciki a jikinta don wani dan ya cewa da ta yi da wani shirtaccen kyau da ta kara, nonuwanta sun sake cikowa suna tsaye kyam da su. Haidar yana ji da ita yana lailanta duk da canjawar da jawahir ta yi hakan bai sa Haidar ya gano ajiyar da ya yi a jikinta ba, bare ita da kuruciya ta yi mata yawa ita dai tana jin canji a jikinta amma bata dauke shi a komai ba, bare ta kula. Suna ta shirye shiryen dawowa gida sun sayi tsaraba ta 'yan uwa da abokan arziki kamar masu shirin bude kamfanin sutura, da kayan kyale kyale. Jawahir tana kwance lamo a kan gado zazzabi ne me zafi ya rufe ta lokaci daya Haidar ya shigo ya zauna gefen gadon yana cewa kasa uwar bacci ba dai daga wannan 'yar fitar tawa har kin koma baccinba.? Ya sa hannu zai dago ta ya ji jikinta da zafi. A gigice ya dako ta ya rungume ta a jikinsa yana jero mata tambayoyi "Bebina me ya same ki daman vaki da lafiya, baki gaya min ba daurewa kawai kika yi?" Bai jira amsar ta ba ya sabe ta a kafada ya yi waje da ita, motar Hotel din ya yi amfani da ita ta xuwa asibitin. Likita Bilkisu muhd Adam ta karbe ta cikin gaggawa ta shiga yi mata tambayoyi da gwaje gwaje a lokacin ta yi mata sukanin ta hango karamin ciki dan wata uku a jikinta. Haidar ya juyo cikin farin ciki ya dako kan jawahir yasa harshensa yana lashe hawayen nata. Yasa hannunsa kasar mararta yana dan shafawa ya rada mata a kunnenta babyna mu duka mun yi kuruciya da wauta sai dai mu kiyaye gaba sai dai mi ta addu'a Allah ya raya mana Bebinmu Allah ya fito mana da shi lafiya." Ta ce, "Amin cikin shagwaba ta ce ka huce my love." Ya sake rungumarta na hakura bebina tun da ke ma ba laifinki ba ne na mune da rashin kulawarnu. Nan fa sabon tattali da ririta suka tashi don Haidar daga kansa yake yiwa jawahir wanka wai don kada ta wahala duk wani abu da take yi masa yanzu shi ya dauke mata nauyinsa. Ita kuma ta kan shagwabe masa ta ce yana ta aikin lada haka yake so ta zauna ba nono. Ya ce "Ai aikin lada da yawa yi min kiss shima lada zaki samu. Ya turo mata kumatu ta cije shi ya da fe wajen a'a a'a bazan yarda ba sai na rama. Da ya yi kanta zai turmusheta sai ta daga hannu sama tana cewa bebinka bebinka zaka wahalar dashi ya yi dariya ya dumgure ta." Ta yi dariya don Allah yaya mu goma gida mana. Ya zaro ido "Ke yaushe zan yarda mu shiga jirgi da wannan dan ta yin cikin nawa." Salon kisa wabi abun ya faru da shi ai mu da mu koma gida sai kin haihu su ganmu da bebinmu. Ta marairaice ta fada jikinsa ta saka kuka ya dagota yana dariya to to sarkin shagwaba yi shiru da gangan nake yi rana ita yau jirgin mu zai daga zuwa Nigeria Ta kuma kankame shi tana kyal kyala dariya, Haidar ya gama luguiguita jawahir dukjansu zube a gado suna mayar da numfashi. Hannun Haidar yana kasan marar jawahir yana shafa bebinsa. Ya ce ko kin san wani abu? Ta girgiza kai ya ce sai da likitan nan ta fara gaya min kina da cikinsa nan na gani alamomin hakan daga jikinki. Ga shi yanzu har ya fara fitowa kamar ba dan wata hudu ba, ta marairaice murya cikin shagwaba ta ce wallahi ni kunya nake ji su ganni da cikib nan ai sai suce vani da kunya daga zuwa jinya, na koma da dan rakiya. Haidar ya dada jawo ta jikinsa yana shafa bayinta tare da dariya yace in banda abinki ni shi ne shedar na warke. "Kinga duk wanda ya kalle ki ba sai ya tambaye mu an samu nasarar aiki ko ba'a samu ba, ta dada shigewa jikinsa ta ce yanzu shi kenan kowa yasan abin da muka yi ko? Ya kara tun tsirewa da dariya yanzu bebina in banda abin ki akwai wanda ya taba sha a ruwa ne?" Kowa kika ganshi da ciki ai ta haka ya samu ta ce "Na shiga uku yanzu momyna da Dadyna da Anty da Inna da Abbanka haka za su ganni da ciki gaskiya zan sha kunya kai ku wa ka yi min wayyo babu ruwanka ko? Washegari jirginsu ya daga zuwa Nigeria da yake an san da dawowarsu 'yan uwa iyayensu sun zo taryarsu babu wanda yasan jawahir tana da ciki sai dai idonsu ya gane musu. A cikin jirgi, jirgi yana jama'a aka fara sakkowa, Haidar ne a gaba jawahir tana biye da shi sun yi kyau sun dade kara ja da fari jin dadi da hutu ya sa sun haske wajen kowa ya kalle su sai ya sake duban su ba don murmushin da su ke dokawa ba, da iyayensu basu gane su ba. Suna sakkowa jawahir zata kwasa da gudu ganin iyayenta Haidar ya riko ta yana ce matw ki kula kada ki yi min ganganci da ciki." 'Yan uwa suka yunkuro gaba daya suka taro su jawahir ta durkusa kasa ta kama kafar babanta ta rike tana me jin dadi da murnar ganinsu. Ya sa hannu ya dagota yana kallonta fuskarsa cike da murmushi na yanda yaga 'yarsa ta kwantar da hankalinta gashi yanda ta kara kyau da haske kamar balarabiya. Inna ta dafa kafadarta jawahir ta juyo ta rungume ta tana murna Inna ta dako ta cikin dariya ta ce ke taurin me nake ji haka? Ko dai kin samo mana dan London? Kai amma abu ya yi kyau." Dady ya ce "Menene?" Inna ta ce, "Ciki ne da ita da sauri jawahir ta fuzge jikinta cikin jin kunya taje ta rungume Mominta da Antinta, ta je ta gaisa da Abban Haidar. Nan fa sukai ta gaisawa da 'yan uwa ana murnar ganin juna. Daga nan suka rankaya gaba daya don raka su gidansu. Jawahir ta yi mamakin canja fasalin gidan nasu da aka yi, ya yi masifar tsaruwa, don ya fi na da ma kyau, tsadaddun kujerun da kayan kyale kyalen da suka suyo a kasar waje. An kawata babban falon da su, sai ka ce falon sarauniya America don tsananin tsaruwa da kyau da ya yi sai da aka ci aka sha sannan iyayensu suka taya su murnar samun lafiyar. Haidar da karuwar da suka samu. Kowa ya fashe, sun tattafi ma'aikatan gidan suka kara gyara gidan ko ina ya kara yin fes sai sheki da kyalli ne yake tashi da hadadden kamshi. Da daddare "Faruk ya zo suka rungume juna shi da Haidar suna murnar sake ganin juna. ❤❤❤SALON SO❤❤❤ ❤❤❤ PART 37 ❤❤❤ . By Sulaiman Bomboy. . Jawahir ta shigo masa da kayan ciye ciye suka shiga gaisawa. Faruk ya ce "Mutumin lallai naga alamar ka warke har da tsarabar dan london ne ko jafan ko dan ijift ne ko America? Naga alamar kamar jawahir tana da ciki ko?" Haidar ya yi dariya ya ce "Ai ma ganinku nayi masu tambaya yanxu kuwa kowa ya kalle ta yaga shedar aiki ya yi kyau. Suka kyalkyale da dariya tare da tafawa Faruk ya ce, "Bakinmu da nayi muku dai ya kama ku to Allah ya raba lafiya, Ubangiji ta sa masu amfani ne ya bamu masu albarka, don Hafsat tana can da nata tsohon cikin. Kai mutumin lallai kayu aiki, to Allah ya inganta mana, Ubangiji ya raba su lafiya da shi. Bayan sun nutsu sun huta suka bude tsarabobi suka rinka bin 'yan uwa da dangi suna rabo kowa aka bashi tsaraba sai ya jinjina kudin da aka kashe masa. Jikaken abu mai muhimmanci da tsaraba da mutum sai yaga kamar shi suka yiwa tafiyar. Anty Maryam ma da Uncle har gida suka zo yi wa su jawahir barka da kuma yi musu sannu da zuwa. Da yake hutun su suka dakko zasu dade a nan a gidan Ankul din suke zaune wanda ya zauna farkon aurensa kafin aiki ya maida shi Abuja. Jawahir ta sha murna da ganin Antyna Maryam ta rungume ta suna ta dariya cikin jin dadi da walwala kamar sa hadiye junansu. Anty ki ce kin kusa haihuwa don naga cikin naki ya yi tsini da yawa." Ta ce "Haka Ankul dinki yake cewa wannan cikin ya fiye girma da yawa wai yana takura shi don na fiye langwai. Jawahir tasa dariya ai gaskiya Anty sai yanzu na gano sirrin da ya sa Ankul ya ke manne miki ko, na ce ku ke manne wa juna, ashe haka rayuwar aure take? Hakika jawahir rayuwar aure aba ce mai dadi da nishadantarwa kwanciyar hankali da samun nutsuwa. Amma fa duk wa 'yannan abubuwan basa samuwa sai ka yi da ce da abokin rayuwa nagari." Haidar ya yi sallama ya shigo tare da cewa da Maryam "Antynmu ai kin yi nauyi da yawa, da kin hakura da zuwan da sai muzo har gida mu gaishe ku." Ta yi dariya tare da cewar ai bazan iya jure rashin ganin diyata ba, yanda ake yi min zuzutun kara kyan da tayi amma da nazo ai na gani idona ya gane min kyakkyawar kulawar da ka yi ma 'yata. Ya yi murmushi ya kalli jawahir ya ce, "Bebina zamu fita da Ankul xuwa dare zamu dawo." Ta marairaice fuska kamar mai shirin kuka ya dafa ta "Haba bebina mene ne kuma bana so ki bata ranki, ba ga Antynki nan zata taya ki hira ba, sai mun dawo zai dauke ta su ta fi. Ta yi murmushi yayin da ta juyo ta kalli Anty maryam. Ta ga ita ba ta saurari su ma, hankalinta yana kan littafi tana karantawa. Haidar ya riko ta suka yo falon tsakiya ya zauna a kujera ya dorata kan cinyarsa "Meye damuwarki babyna? Ta yi rau rau da ido har sunkawo kwalla ta ce "Ni ba komai va ne ina tsoron kada Ankul ya sake cewa ka dawo da Kausar ne, ba zan jure ganin kana yi mata magana ba bare har ka shiga dakinta ka kwana mun zama mu biyu da matsayi daya a wajenka ta saki kuka. Haidar ya rungume ta yana rarrashinta. "Kar ki damu Bebyna, daman can kaddara da sha'awar kare kaina daga zina ita ta sani auren Kausar, ki sa a ranki tsakanina dake mutu ka raba ne takalmin kaza aurenmu auren zobe ne ba saki ba yaji ba kishiya har avada. Kuma na ji wai SULAIMAN BOMBOY za ta aura. Ta ce, "waye kuma SULAIMAN BOMBOY?" Ya ce wani yaro ne dan karami amma ya nace wai shi a lallai sai ita. Ta ce, "Um. Ta dako kai da sauri "Allah yayana? Ya ce, "Sosai ma kuwa ta yi saurin kankame shi tana sumbatarsa, cikin murna ya dako ta yana dariya muje kada Ankul ya gaji da jira. Suka fito babban falo jawahir ta ce "Ankul ka bar min Anty ta kwanar min anan." Ankul ya girgiza kai ya ce, jawahir kenan har yanzu dai kina tare da kuruciya, to idan haihuwa tazo kuma cikin dare ku yi yaya da ita, ku da kuke duk farin shiga? Gaba daya suka sa dariya suka fice ita kuma ta koma gun Anty maryam suka bude shafin hira. "Kin gane ne Anty ni fa yanzu abun da nake tsoro kada Haidar ya dawo da kausar don ban san yanda zan yi ba, a da ban damu da aurenta sosai ba don sannan ban damu da Yayan ba, amma anya yanzu yanda nake son Yaya Haidar muka shaku da shi yake sona yana ririta ni yana tarairayata kamar kwai, zan juri ganinshi da wata matar, wai! Naga mace a rungume a kirjin Haidar, subhanallahi Allah ma ya kiyaye, Anty ai wuka zan soka mata ta mutu nan take. Maryam ta tuntsire da dariya ta ce "Allah ya kiyaye jawahir," Anty maryam ta ce "Ai na gaya miki wasu matan su suke jawowa kansu ake yo musu kishiya, na farko akwai matan da girman kai da ji da kai tsabagen muskilanci ya yi musu yawa, to yawanci masu irin wannan halin sai ki ga har mazajensu na aure su ke yiwa ko suna mantawa a karkashin mazajen su suke? Dole mazan su ne gaba da su, dole ne duk matsayinki da jin kanki, ki sauke su ki yiwa mijinki biyayya ko dan ki samu tsira ma ranar gobe kiyama, domin aljannar mace ta na tafin kafar mijinta sai ya daga zaki shiga. Abu na biyu kuma shine, kazanta, sai ki ga mace awaje dagwas dagwas da ita amma da zarar ta yi aure ta haihu sai kiga ta zama kazama. Ba za ta tsaya ta tsabtace kanta ba bare abincinsu ko abin shansu. Wasu matan za ki ga kudin da aka ba su na cefane a ciki zasu raga su boye baza su yo cefanan na duka ba bare su sarrafa girkin yanda zai yi dadi. Sai mace tai abinci garau garau ba wadataccan kayan miya bare mai kiji abinci kadas babu dadi abinci babu kyau a fuska. Bayan ta gama girkin ba ta san tai wanka ba ta gyara jikinta, a'a sai ki ganta daga ita sai daurin kirji tana ta fama da kaurin wuta. Da kin doshi dakinta sai zarnin fitsarin da warin dauda. Kin kai wa namiji abinci ya yi cokali biyu ko uku ya ji ya kasa ci ya ture saboda rashin dadi. Baruwanki da kwantar da murya bare ki bincike shi me ya hana shi cin abincin, a'a ke babu ruwanki sai ki ja kwanon gabanki ki kama ci ko ki kirawo yaranki ki ce kuzo ku dau abinci babanku ya rage, babu ruwanki da damuwarsa. Idan dare ya yi kina kwance cikin yaranki kin saki baki kina munshari kin bude nono kin saka wa yaron da kike goyo a baki kin riga kin sabar masa, sai da nono a bakinsa zai yi bacci, da maigidanki ya zo ya taba ki don ki taso yana da bukatarki ki kama miya kina faman zumburar baki ke an takura miki kin gaji, daren ma ba za'a barki ki huta ba, saboda Allah mijin nan naki waliye ne da ba zai bukataci mace ba in har Allah ya kare shi daga sharrin zina? Ai kuwa dole ya yi kokarin karo aure ko dan ya samu me debe masa sha'awa. Jawahir ta ce, "Yanzu Anty kina ganin wa'yannan dalilai zasu taimaka wajen yo wa mace kishiya? Anty maryam ta ce "Kwarai kuwa ai wadannan su ne kan gaba, idan mace ta zamo bata daraja mijinta bata ganin mutuncin iyayensa tana wulakanta masa 'yan uwa da abokanan arzikinsa to yana kara aure gudun kada ta rusa masa zumunci da 'yan uwansa. Jawahir ta ce, "To ai Anti in kika yi la'akari da wasu mazan kwata kwata ba su san darajar mace ba, sun dauki mace baiwarsu abar korewa sha'awarsu, don wani namijin zaki ga namiji yana wasa da dariya a waje ki ga yana tayiwa 'yan mata fara'a yana jansu da wasa, amma da zarar ya shiga gidansa sai ki ga ya koma kamar mala'ikan mutuwa ya murtuke fuska babu alamar fara'a bare wasa, da ya ci karo da kwano ko wani abu nata akan hanya zai bal da shi, kuma yana da rufin asirinsa amma sai ya ba wa iyalansa dan kalilan din kudin da ba za su wadaci girkin gidansa ba, ba ruwansa bai damu da matsalar da suke ciki ba, bai ja su a jikinsa ba, bare su saki jiki da shi har su dinga bayyana masa damuwarsu. Anty duk irin wannan ai rashin adalci ne da sanin darajar mace ko? Anty maryam ta ce "Haka ne jawahir amma ni a ganina idan Allah ya hada ka zama da irin wa'yannan mazan to sai ka iya zama da su. Na farko mace ta dasa wa zuciyarta hakuri, ta zamo mai juriya da tawakkali, na biyu ta kasance me yawan ibada tai ta addu'a tana kai kukanta ga Allah, na uku ta samu sana'a komai kankantarta kada ta raina ta ta rike ta hannu biyu. Na hudu ta zamo mai kyautata masa da yi masa biyayya ko dan ta samu tsira ranar lahira. Na biyar ta kasance me tsafta da kwalliya da kasancewa cikin kamshi. Na shida ta kasance cikin koyon iya kissa da kwantar da kanta tana kaskantar da kanta ko yaushe tana nuna masa shi ne sama da ita, na bakwai ta kasance doluwa marar wayo ta zamo me kau da kai da duk wani abu da zai mata, na takwas ta zamo mace me iya kula da rayuwarta wato tana cin abubuwan da za su kara mata ni'ima a jikinta. Na tara mace ta iya kwanciyar aure ta gano wace irin kwanciyar aure mijinta ya fi bukata, me da me da me mijinta ya fi sha'awa a jikin mace, sai ta rinka gyara nata yanda zai rinka daukar hankalinsa yana bashi sha'awa ba tare da na mace daban ya burge shi ba. ❤❤❤SALON SO❤❤❤ ❤❤❤ PART 37 ❤❤❤ . By Sulaiman Bomboy. . Jawahir ta shigo masa da kayan ciye ciye suka shiga gaisawa. Faruk ya ce "Mutumin lallai naga alamar ka warke har da tsarabar dan london ne ko jafan ko dan ijift ne ko America? Naga alamar kamar jawahir tana da ciki ko?" Haidar ya yi dariya ya ce "Ai ma ganinku nayi masu tambaya yanxu kuwa kowa ya kalle ta yaga shedar aiki ya yi kyau. Suka kyalkyale da dariya tare da tafawa Faruk ya ce, "Bakinmu da nayi muku dai ya kama ku to Allah ya raba lafiya, Ubangiji ta sa masu amfani ne ya bamu masu albarka, don Hafsat tana can da nata tsohon cikin. Kai mutumin lallai kayu aiki, to Allah ya inganta mana, Ubangiji ya raba su lafiya da shi. Bayan sun nutsu sun huta suka bude tsarabobi suka rinka bin 'yan uwa da dangi suna rabo kowa aka bashi tsaraba sai ya jinjina kudin da aka kashe masa. Jikaken abu mai muhimmanci da tsaraba da mutum sai yaga kamar shi suka yiwa tafiyar. Anty Maryam ma da Uncle har gida suka zo yi wa su jawahir barka da kuma yi musu sannu da zuwa. Da yake hutun su suka dakko zasu dade a nan a gidan Ankul din suke zaune wanda ya zauna farkon aurensa kafin aiki ya maida shi Abuja. Jawahir ta sha murna da ganin Antyna Maryam ta rungume ta suna ta dariya cikin jin dadi da walwala kamar sa hadiye junansu. Anty ki ce kin kusa haihuwa don naga cikin naki ya yi tsini da yawa." Ta ce "Haka Ankul dinki yake cewa wannan cikin ya fiye girma da yawa wai yana takura shi don na fiye langwai. Jawahir tasa dariya ai gaskiya Anty sai yanzu na gano sirrin da ya sa Ankul ya ke manne miki ko, na ce ku ke manne wa juna, ashe haka rayuwar aure take? Hakika jawahir rayuwar aure aba ce mai dadi da nishadantarwa kwanciyar hankali da samun nutsuwa. Amma fa duk wa 'yannan abubuwan basa samuwa sai ka yi da ce da abokin rayuwa nagari." Haidar ya yi sallama ya shigo tare da cewa da Maryam "Antynmu ai kin yi nauyi da yawa, da kin hakura da zuwan da sai muzo har gida mu gaishe ku." Ta yi dariya tare da cewar ai bazan iya jure rashin ganin diyata ba, yanda ake yi min zuzutun kara kyan da tayi amma da nazo ai na gani idona ya gane min kyakkyawar kulawar da ka yi ma 'yata. Ya yi murmushi ya kalli jawahir ya ce, "Bebina zamu fita da Ankul xuwa dare zamu dawo." Ta marairaice fuska kamar mai shirin kuka ya dafa ta "Haba bebina mene ne kuma bana so ki bata ranki, ba ga Antynki nan zata taya ki hira ba, sai mun dawo zai dauke ta su ta fi. Ta yi murmushi yayin da ta juyo ta kalli Anty maryam. Ta ga ita ba ta saurari su ma, hankalinta yana kan littafi tana karantawa. Haidar ya riko ta suka yo falon tsakiya ya zauna a kujera ya dorata kan cinyarsa "Meye damuwarki babyna? Ta yi rau rau da ido har sunkawo kwalla ta ce "Ni ba komai va ne ina tsoron kada Ankul ya sake cewa ka dawo da Kausar ne, ba zan jure ganin kana yi mata magana ba bare har ka shiga dakinta ka kwana mun zama mu biyu da matsayi daya a wajenka ta saki kuka. Haidar ya rungume ta yana rarrashinta. "Kar ki damu Bebyna, daman can kaddara da sha'awar kare kaina daga zina ita ta sani auren Kausar, ki sa a ranki tsakanina dake mutu ka raba ne takalmin kaza aurenmu auren zobe ne ba saki ba yaji ba kishiya har avada. Kuma na ji wai SULAIMAN BOMBOY za ta aura. Ta ce, "waye kuma SULAIMAN BOMBOY?" Ya ce wani yaro ne dan karami amma ya nace wai shi a lallai sai ita. Ta ce, "Um. Ta dako kai da sauri "Allah yayana? Ya ce, "Sosai ma kuwa ta yi saurin kankame shi tana sumbatarsa, cikin murna ya dako ta yana dariya muje kada Ankul ya gaji da jira. Suka fito babban falo jawahir ta ce "Ankul ka bar min Anty ta kwanar min anan." Ankul ya girgiza kai ya ce, jawahir kenan har yanzu dai kina tare da kuruciya, to idan haihuwa tazo kuma cikin dare ku yi yaya da ita, ku da kuke duk farin shiga? Gaba daya suka sa dariya suka fice ita kuma ta koma gun Anty maryam suka bude shafin hira. "Kin gane ne Anty ni fa yanzu abun da nake tsoro kada Haidar ya dawo da kausar don ban san yanda zan yi ba, a da ban damu da aurenta sosai ba don sannan ban damu da Yayan ba, amma anya yanzu yanda nake son Yaya Haidar muka shaku da shi yake sona yana ririta ni yana tarairayata kamar kwai, zan juri ganinshi da wata matar, wai! Naga mace a rungume a kirjin Haidar, subhanallahi Allah ma ya kiyaye, Anty ai wuka zan soka mata ta mutu nan take. Maryam ta tuntsire da dariya ta ce "Allah ya kiyaye jawahir," Anty maryam ta ce "Ai na gaya miki wasu matan su suke jawowa kansu ake yo musu kishiya, na farko akwai matan da girman kai da ji da kai tsabagen muskilanci ya yi musu yawa, to yawanci masu irin wannan halin sai ki ga har mazajensu na aure su ke yiwa ko suna mantawa a karkashin mazajen su suke? Dole mazan su ne gaba da su, dole ne duk matsayinki da jin kanki, ki sauke su ki yiwa mijinki biyayya ko dan ki samu tsira ma ranar gobe kiyama, domin aljannar mace ta na tafin kafar mijinta sai ya daga zaki shiga. Abu na biyu kuma shine, kazanta, sai ki ga mace awaje dagwas dagwas da ita amma da zarar ta yi aure ta haihu sai kiga ta zama kazama. Ba za ta tsaya ta tsabtace kanta ba bare abincinsu ko abin shansu. Wasu matan za ki ga kudin da aka ba su na cefane a ciki zasu raga su boye baza su yo cefanan na duka ba bare su sarrafa girkin yanda zai yi dadi. Sai mace tai abinci garau garau ba wadataccan kayan miya bare mai kiji abinci kadas babu dadi abinci babu kyau a fuska. Bayan ta gama girkin ba ta san tai wanka ba ta gyara jikinta, a'a sai ki ganta daga ita sai daurin kirji tana ta fama da kaurin wuta. Da kin doshi dakinta sai zarnin fitsarin da warin dauda. Kin kai wa namiji abinci ya yi cokali biyu ko uku ya ji ya kasa ci ya ture saboda rashin dadi. Baruwanki da kwantar da murya bare ki bincike shi me ya hana shi cin abincin, a'a ke babu ruwanki sai ki ja kwanon gabanki ki kama ci ko ki kirawo yaranki ki ce kuzo ku dau abinci babanku ya rage, babu ruwanki da damuwarsa. Idan dare ya yi kina kwance cikin yaranki kin saki baki kina munshari kin bude nono kin saka wa yaron da kike goyo a baki kin riga kin sabar masa, sai da nono a bakinsa zai yi bacci, da maigidanki ya zo ya taba ki don ki taso yana da bukatarki ki kama miya kina faman zumburar baki ke an takura miki kin gaji, daren ma ba za'a barki ki huta ba, saboda Allah mijin nan naki waliye ne da ba zai bukataci mace ba in har Allah ya kare shi daga sharrin zina? Ai kuwa dole ya yi kokarin karo aure ko dan ya samu me debe masa sha'awa. Jawahir ta ce, "Yanzu Anty kina ganin wa'yannan dalilai zasu taimaka wajen yo wa mace kishiya? Anty maryam ta ce "Kwarai kuwa ai wadannan su ne kan gaba, idan mace ta zamo bata daraja mijinta bata ganin mutuncin iyayensa tana wulakanta masa 'yan uwa da abokanan arzikinsa to yana kara aure gudun kada ta rusa masa zumunci da 'yan uwansa. Jawahir ta ce, "To ai Anti in kika yi la'akari da wasu mazan kwata kwata ba su san darajar mace ba, sun dauki mace baiwarsu abar korewa sha'awarsu, don wani namijin zaki ga namiji yana wasa da dariya a waje ki ga yana tayiwa 'yan mata fara'a yana jansu da wasa, amma da zarar ya shiga gidansa sai ki ga ya koma kamar mala'ikan mutuwa ya murtuke fuska babu alamar fara'a bare wasa, da ya ci karo da kwano ko wani abu nata akan hanya zai bal da shi, kuma yana da rufin asirinsa amma sai ya ba wa iyalansa dan kalilan din kudin da ba za su wadaci girkin gidansa ba, ba ruwansa bai damu da matsalar da suke ciki ba, bai ja su a jikinsa ba, bare su saki jiki da shi har su dinga bayyana masa damuwarsu. Anty duk irin wannan ai rashin adalci ne da sanin darajar mace ko? Anty maryam ta ce "Haka ne jawahir amma ni a ganina idan Allah ya hada ka zama da irin wa'yannan mazan to sai ka iya zama da su. Na farko mace ta dasa wa zuciyarta hakuri, ta zamo mai juriya da tawakkali, na biyu ta kasance me yawan ibada tai ta addu'a tana kai kukanta ga Allah, na uku ta samu sana'a komai kankantarta kada ta raina ta ta rike ta hannu biyu. Na hudu ta zamo mai kyautata masa da yi masa biyayya ko dan ta samu tsira ranar lahira. Na biyar ta kasance me tsafta da kwalliya da kasancewa cikin kamshi. Na shida ta kasance cikin koyon iya kissa da kwantar da kanta tana kaskantar da kanta ko yaushe tana nuna masa shi ne sama da ita, na bakwai ta kasance doluwa marar wayo ta zamo me kau da kai da duk wani abu da zai mata, na takwas ta zamo mace me iya kula da rayuwarta wato tana cin abubuwan da za su kara mata ni'ima a jikinta. Na tara mace ta iya kwanciyar aure ta gano wace irin kwanciyar aure mijinta ya fi bukata, me da me da me mijinta ya fi sha'awa a jikin mace, sai ta rinka gyara nata yanda zai rinka daukar hankalinsa yana bashi sha'awa ba tare da na mace daban ya burge shi ba. SALON SO PART 38 . BY SULAIMAN BOMBOY . Abubuwan da mace zata ci su kara mata ni'ima ba lallai sai ta fitar da kudinta ta sai masu tsada ba, a'a daidai ruwa daidai tsaki, kada ki ce to ke ma ina kika ga kudin bayan ba baki yake yi ba, ke ba wani abu da za ki siya don gyara kanki. To gaskiya wannan rashin wayo ne ai kan ki zaki gyara duk sanda namiji ya kusance ki ya ji ki zam zam da ke, tsindum da ke dole ne ya rinka tattalinki ya na baki kyakkyawan kulawa saboda yana son biyan bukatarsa. Amma ke baki gyara kanki va, kin zauna gundin murhu duk wuta ta kone miki dan ruwan da yake jikinki, mijinki ya zo ya ji kamas, saboda Allah me kike ganin zai faru? Dole darajarki ta ragu idonsa, amma idan kika dage da shan su lemo, kankana, rake, aya gwanda, ayaba, dabino, cukui, inibi, zogale, zaitun, tumatur, kwakwa, zuma, nono, madara, gurji, dafaffiyar gyada, da sauransu duk irin wannan ba karamin taimaka mana suke ba na kara mana ni'imar jikinmu. Ko nera koma ki ka bayar a siyo miki dan kifi ki yi romonsa da kayan kanshi da alvasa da tumatur kika watsa wake a ciki ya dahu luguf da dan alaiyahu ki yi shi romo romo shi ma yana taimakawa, ki sami danyar gyada gwangwani daya, aya gwangwani daya, waken suya gwangwani daya, alkama gwangwani daya, ki hada ki jika a markado miki ki ta ce shi kamar gasara ki rinka damawa kina sa madarar ruwa kina sha za ki ga yanda zai taimaka miki ya sakar miki da ni'ima a jikinki. Kinga abu mafi sauki idan kika sami ayarki kika jikata ta juku ki ka kai markade kizo ki tace kayarki ki kara sikari ki rinka sha zata kara miki ni'ima sosai. To kinga iri iren abubuwan nan idan mace tana yi zata taimaka wa kanta don kare wulakancin namiji. To idan kuma ta iya gamsar dashi ta san sirrika na iya kwanciya da da namiji to zata mallake shi a hannunta har a rinka zargin ta asirce shi ne. Jawahir ta ce, "To Anty me zai hana murubutanmu ba za su rinka wayar wa da mutananenmu kai ba, ko dan sanin irin wannan sirrikan kwanciya don su ma su mallaki mazajensu a hannu a daina yawan mutuwar aure? Maza su daina fita bariki neman matan banza su rinka tsayawa iya matansu na sunna kawai? "To ai jawahir matsalar da ake samu kin gane ne, marubutanmu suna iya bakin kokarinsu na ganin cewar sun ganar da yawancin mutane yanda rayuwar jin dadi ta aure take, to amma kash! Wani abu da ake kuka dashi wai sai ace suna bata tarbiyar yara, wai yara kanana suna diban lattattafai suna karantawa, suna ganin abin da bai kamata ba, wanda gaskiya ni kuma ina ganin ba haka ba ne, domin idan kinga yarinya ta lalace to dama can lalatacciyarce iyaye suna ina 'ya 'yansu suke fita su shiga gidan amare su rufe kansu suna ganin kaset din blue film ko America, ko ibo, ko fim din Turawa da yake bayyanar da tsiraici karara da yanda ake nuna soyayya ta kazamar hanya. Wasu ma tare da samari suke gani to meye ma ba zai faru ba wajan wannan kallon wa'yansu yaran kuma da ake batawa ba su da wayewar kan ma da za su yi karatun littafin ake jansu ayi musu fade, shi kenan hanyar lalacewarsu ta samu. Wasu yaran kuma rashin kulawa ta iyaye da rashin sa ido akan harkokin su ne yake jawo hakan, wasu tsabagen kwadayi ne da rashin kamun kai da zubar da tsantsar da darajarsu ta 'ya 'ya matar ne take jawowa. Gaskiya bazan taba yarda ace wai karatun littafi yana sa 'yan mata suna lalacewa ba, saboda duk wata mace da ta san darajar kanta to in har ta karanta littafi ina ganin zata yi kokarin kare mutuncin kan ta ta yi kokarin kai budurcinta gidan mijinta, saboda ta karanta littafi taga yanda daren farko ya kasance ga yarinyar littafin, mijinta ya same ta a cikakkiyar mace ta ga irin tarairaya da Kulawar da yake bata taga yanda yake sa mata albarka har da wata dunkuleliyar kyauta da ya yi mata, to ni a ganina kowace budurwa zata yi sha'awar hakan har ta yi kokarin kai budurcinta gidan mijinta Abu na biyu 'yan matanmu za su iya koyon kissa da shagwaba da kalolin girke girke da yanda ake tarairayar namiji, zasu san abubuwan da suke kara wa mace ni'ima wanda za su fara tsuma kansu tun kafin su shiga gidan auren, domin idan ba'a littafin ba babu in da za su sami hakan saboda al'adar Bahaushe da kunya babu uwar da zata iya zaunar da 'yarta ta koya mata wa'yannan abubuwan don zata yi mata aure, za dai ayi wa 'ya fada ki bi mijinki ki yi masa biyayya, to kin je kina ta biyayya yana wulakantaki ke baki san dalili ba to duk wa'yannan abubuwa ne da bakya yi, amma aure ya samu tattali kissa biyan bukata, shagwaba, ladabi da biyayya, iya girki, iya kwanciya, amfani da turaruka masu kamshi da na tsugunno, ta cikin ikon Allah za'a samu zaman lafiya da fahimtar juna a cikin aure. Shi turaren tsugunno ana amfani da shi ne wajen turare gabanka ka tsugunna akai hayakin yana shiga ciki to yana kara hade mace ne ya matse ta kamar amarya. Jawahir ta kawo gauron numfashi ta ce, "Anty na fahimce ki Allah ka ganar da yawancin al'umma ko a sami zaman lafiya a tsakanin ma'auratnmu" "To amin Jawahir." Ba jumawa Haidar da Ankul suka dawo suka ci abinci. Ankul ya ce da Anty maryam ta tashi su tafi gida akwati guda jawahir ta yo wa Anty na tsaraba ta dakko ta kawo mata suka rinka godiya tare da sa albarka. Sai da Haidar da jawahir suka yi sati biyu a gidansu suna hutawa basu da aikin yi sai wasanni da junansu su ci cima me kyau su sha me kyau suke ta sutura me tsada su bada kamshi su manne da junansu suna faranta ran juna. Yau sun cika sati biyu da dawowa don haka yau Haidar ya fara fita xuwa office, jawahir duk ta damu kamar wanda zai je ya yi kwanaki a can sai da ya lallabeta har da yi mata wayo sannan ya fice. Da yake ya dade rabonsa da office din dole ya samu ayyuka kaca kaca sun yi masa yawa shi yasa bai samu sukuni ba, sai na fadawa aiki kawai. Haidar yana tafiya kuwa jawahir ta dauki mota ta tafi wani hadadden gidan gyaran jiki tsadadde na 'ya'yan wane da 'ya'yan wance, aka yi mata gyaran gashi aka gyara mata farce aka wanke kafar aka rangada mata kunshin fulawa. Jikinta ya sha dulka da halawa, jikinta da fuskarta sai wani santsi da taushi yake yi kamar auduga yana fitar da wani sihirtacce na kyau. Tana komawa gida kicin ta shiga ta feraye doya ta dora a wuta ta debo manyan busashen tarwada ta farke cikinta ta kan kare ta kwara masa ruwan zafi. Ta hade markade iya ta yi mata abu landa doyar ta dahu ta tsame ta mika wa iya ta daka mata sakwara, ta hade miyar busashen kifin nan da ta ji onga, kori, reko, mai da sauren kayan da su ke sa girki armashi, sannan ta cuko zallar tsokar nama a firinji ta tafasa shi da albasa gishiri da dan magi. Bayan ya tafasa ta kwankwatsa attaruhu albasa ta dakko tafasashen naman nan ta hada a turmi ta daka. Ta ciro shi ta rinka dunkulawa ta fasa kwai ta zuba gishiri onga reko ta dora manta a wuta ya dau zafi ta rinka daukan dunkulan naman nan tana tsoma sha a rwan kwan tana sa wa a manta na soyawa, ta gama wannan ta zo ta yanka salak ta yi masa wanki sosai ta zuba a filet, ta yanyanka tumatur da albasa ta gewayesu a saman salak da albasar ta kawo dafaffiyar hantarta da ta yi mata kananan yanka ta zuba a kai. Bayan ta yada salak, cream ta zuba heinze beans a tsakiya duk wanda ya kalli hadin salak din dole yawunka ya tsinke, ta debo kayatattun fulas dinta ta zuba komai taje ta jere su a santara tebir. Ta debo fararen gobarta manya ta markada ta tace dusar ta markada kankana da gwanda da ayaba a duk ta tace dusar ta hada akan ruwan gwaibar, ta daddara rake ta matse ruwan ta hada akai, ta zuba ruwan kwakwa da ruwan markadaddiyar aya ta zuba madarar ruwa gwangwani biyu ta kawo zumarta me kyau ta zuba a ciki ta juya ta saka a firinji. ❤❤❤SALON SO❤❤❤ . ❤❤❤ PART 39 ❤❤❤. .. By Sulaiman Bomboy. . "Subhanallahi! Lallai jawahir kin hada kyakkywan lemo mai saurin saukar da ni'ima a jikin ta bar wa iya rama ita kuma ta kara gyara falon da dakin megida ko ina ta turare shi da daddadan turaren wuta na kamshi kowacce kusurwa ta feshe ta da Air freeshner. Ko ina ta sa ka AC sai sanyin dadi ne yake fita ta gyara toilet ma shima ta turare shi da daddadan kamshi, ta rufe sashinsa ta fito ta sakko ta shiga nata sashen ta sake gyarawa ta saki kamshi ta fada toilet don yin wanka, ta dade tana murzar jikinta da daddadan sabulu ga ruwan wankan nata ya sha turaren wanka sai turarin kamshi ne yake tashi Uku da rabi ta fito daga wanka ta dauro alwala ta zo gaban mudubi ta fara tsara kwalliya shafa nan goge nan ko ina ya yi das, ta fara gabatar da sallar la'asar, ta tsara kwalliya da wani pink din les mara nauyi sai dai anyi masa shafi a ciki, duk da rigar fitet ce ta dan fara kamata ko don cikin jikinta de da ya fara bayyana, duk wata gaba ta jikinta ta mulke ta da turaren kamshi, ta fesa na fesawa ta daura dan kwalin les din ya lafe kan gyaran gashin da ta yi. Gaskiya ta yi kyau wannan da gasar sarauniyar kyau zata je babu abin da zai hanata lashe gasar. Ta dakko turare tana sake fesawa, daidai lokacin da Haidar ya shigo da kyar yake daga kafa don tsananin gajiya da yunwa tun break dan safe. Ya zube a kujerar falo yana mai nishi, "Bebina." "My love." Jawahir ta fito daga cikin daki ta zagayo gabansa idonsa yana limshe kamshin turarenta da ya ji ne ya sa shi bude ido. Subhanallahi, duk kyan jawahir sai yaga yau tafi kullum kyau kamar wata fure aka dasa don kyau tuni gajiyar da ya kwaso ta ware, ya jawo ta cinyarsa yana yi mata wani fitinannen kallo mai tada sha'awa da raunannar zuciyar mai bege. Ta sa hannunta ta rufe masa idon ya ciji hannun nata ta yi saurin janyewa ta langabe kai cikin shagwaba tana 'yar kara tare da yarfe hannun nata. Shikuwa Haidar tuni ya samu damar zira harshensa a kyakkyawan bakinta, ya dade yana sumbarta ta cikin shaukin so da igiyar bege da kyar ta zare jikinta sakamakon wani nishi da ta ji yana yi gudun ka da ta jawowa kanta jan gwam ta yi saurin haye wa samanta ta fada toilet dinsa ta hada masa ruwan wanka, tana fitowa daga toilet din taga ya shigo idon sa duk ya yi ja saboda fitina, ya sake jawo ta ya mannata a jikinsa ya sake rungume ta ta langabe cikin shagwaba take cewa, "My love ka je ka y wankan kai muke jira fa Bebinka be ci abinci ba. Ya yi saurin cika ta ya dago kai yana shafa cikin "Haba don Allah me yasa za ki bar min beby da yunwa kina so ya galabaita ne, taho muje na fara baki abincin tukuna, in kin koshi nayi wankan. Ta make kafada ta ce um um ni dai ka shirya muje mu ci tare. Ya jata ya zaunar da ita a gefen gado, to zauna nan yanzun nan zan fito ba zan dade ba. Ya shige toilet din da sauri ita kuma ta tashi ta dakko masa kayan da zai saka farar shirt ce da bakin wando, ta feshe su da turare bai jima ba ya fito daure da tawul sai wani akansa, ta yi saurin tashi ta ciri tawul din kan nasa ta fara goge masa jikinsa, ta jashi gaban madubi ta shafe masa jikinsa, da lafiyayyan cream me taushi da dadin kamshi, har da shafa masa farar, hoda ta feshe shi da turare ta ware masa kyansa ya karba ya saka. "Au my love na manta ban sa maka man lebe ba" ya sunkuyo da kansa ta shafa masa. "Inye! Nawan ba, ka kara kyau. Ya yi murmushi tare da manna mata kiss a lebe ya riko ta suka taho falo.kasa suka sauko da kayan abincin ya hau kan kafet aka baje don jawahir tafi sakewa. Ta je firji ta tsiyayo hadadden lemon ta a je ya dau sanyi kuwa, ta zo ta ajiye ta dauki babban filet ta bude fulas din ta sako musu sakwarar ta bude miyar yayin da kamshinta ya bugi hancin Haidar ya limshe ido yunwarsa ta dawo sabuwa, ta bude daya filas din shima ta zubo musu hadin curaram naman da ta soya da kwai, ta bude farantin hadin salak ta kalli Haidar ta ce, "My love bismillah. Ya kalle ta yana murmushi sannu bebyna na gode miki Allah ya saka miki da alheri Ubangiji ya yi miki albarka, burinki kullum ki faranta min ki yi min abin da zai sani farin ciki. "To my love in ban yi maka ba wa zan yi wa, ina alfahari, ina matukar farin ciki da baiwar da Allah ya yi min ta haduwa da gwarzon masoyi Suka fara cin abinci dole jawahir ta rinka kyalkyala dariya saboda yanda Haidar ya ta karkare yana ta ziri tare da suba santi. Komai sai da suka ci su ka koshi suka yi kat da su. Jawahir ta rinka tsiyaya wa Haidar hadin lemon yana sha yana zuba santi shi dai ba don ya ji cikinsa yana barazanar fashewa ba da ba zai bar sha haka ba. Jawahir ta kwashe kayan ta mayar kicin Haidar ya jingina da kujera ya mimmike kafa ya dauki romote din tibi yana danne dannan tashoshi. Jawahir ta dawo ta zauna ya juyo ya kalle ta cike da kulawa yana murmushi ya ce, "Ya aka yi ne bebyna? Ta jawo jikinta ta kwanta a cinyarsa cike da sangarta, ya sa hannunsa kasan mararta yana shafawa ya cire dankwalinta yana yaba kyan gashinta ya koma shafa kumatunta yana yaba santsin fatarta da taushin jikinta kamar auduga. Ya dora hannunsa kan kirjinta yana shafawa tare da limshe ido jawahir ta ture hannunsa tare da cewar "Meye haka kake yi a jikin ta tsitsiyar kwaila.?" Ya yi saurin rufe mata baki da nasa ya dinga sumbatarta yana ruda mata jiki da wasanni har sai da ya tabbatar ta manta da maganar tukunna ya cikata. Ikon Allah kenan duk yanda jawahir ta tsani halayyar Haidar ba sa shiri da juna ba sa son junansu, yau ga shi sun fi kowa kaunar junansu. Halayyar Haidar da jawahir ta tsana ta muskilanci da kasaita da jan aji tare da rashin hayaniya ko kwarniya yau tafi kowa murna da alfahari da muskilancin Haidar da daukan kansa hade da isarsa da kasaitarsa. Tun da babu wata budurwa da ta isheshi kallo bare a kai gabatun magana har ya furta mata so, bata isa ba kowacce. So, kauna, aminci, yarda, shakuwa, duk ya tara su ga tauraruwarsa jawahir. Bangaren Haidar kuwa kullum sai ya yi wa iyayensa addu'a da fatan gamawarsu da duniya lafiya saboda yanda suka hada shi aure da jawahir yanda da ya tsani halayyarta ta miskilanci yau ga iyayi shagwaba. Yanzu ga shi sun zamo abin alfaharinsa don suna dada hura wutar kaunar jawahir a zuciyarsa. Hakika ya yi sa'a da ace da samun kammalalliyar mace ga kyau ga tsafta ga addini, ga usuli me kyau. Allah ya yi mata baiwa kala-kala na iya furta kalami wanda lokaci daya zata siye zuciyar mai sauraronta. Abu na biyu ta iya sahirtaccen kallo wanda zai jawo afkawar mutum kogin begenta. Abu na uku ta iya kissa da mutum ya so ta ko da baya ksunarta. Abu na hudu yarinya ce me nutsuwa ga ta da ladabi da biyayya ga hakuri da tawakkali duk ta tara su. Abu na biyar ta iya nau'ika na girki da abubuwan sha ga ta da zakin hannu don duk wanda ya ci girkin ta yai ta zuba santi da ya bawa kenan. Abu na shida ta iya kwalliya gwanace wajen amfani da hadaddun turaruka masu dadin kamshi, da san sutturar da ta dace ta saka kowanne yanayi da kowanne lokaci. Abu na bakwai gwana ce wajen iya tsafta da gyaran gida tun daga dakunnansu falukansu zuwa kicin bandaki harabar gida ko'ina da launin turaren da take kamshinsa da yake yi Abu na takwas ta riga ta gano makamar kama Haidar domin ta fuskanci abin da ya fi so a jikinta wata kirjinta, don haka koda yaushe ta kasance cikin gyara kirjinta tare da sake kaya masu fito mata da surar kirjinta. Abu na tara ta iya tarairayarsa tana ba shi kyakkyawar kulawa ta siye zuciyarsa da kyawawan halayenta, abu na goma na karshe kuma, ta san sirrinkan kwanciya yanda duk yanda ya juyata haka take binsa kowanne kokaci kuma akwai sabon samfarin da zata gudanar masa a makwancinsa. Ba ta gajiya da shi tana dauriya da jure bukatarsa har sai ya gamsu don kanshi ba ta da korafi bare ta nuna gajiyarta, ko ta ce ya fiye fitina Wa'yannan halaye su ne suka ingiza kaunar jawahir take dada ruruwa a zuciyar Haidar. Kwance tashi wajen Ubangiji babu wuya, ga shi cikin jawahir ya shiga wata tara komai na haihuwa sun tanada sai jiran haihuwar kawai suke yi. Wata sabuwar sangarta jawahir take yiwa Haidar saboda ganin yanda take bata tsantsar kulawa. Cikin nata ya yi nauyi duk da haka ba ta yi sakaci da girkin megidan nata ba, bata sakaci duk yanda Haidar ya kai da lallaminta da lallabata baya son yaga tana wani aikin wahala don haka duk safiya yake shiga kicin ya hada musu break. Ya taimaka ma ta ta yi wanka shi yake yi mata kwalliya, ya sa mata kayan da ya san baza su yi mata nauyi a jiki ba, ya rungumo ta zuwa falo kan kafet ya zauna tana rungume a jikinsa yana bata break a baki, sai daki ya kwantar da ita a gado kamar wata jaririy yana yi mata tausa da matsa sannu a hankali sai ya ga ta yi bacci sannan zai shirya ya tafi office. Sha biyu na rana jawahir ta tashi daga bacci sannu a hankali ta mike ta nufi kicin ta fara hada abubuwan da zata dora girki, duk wani yanke yanke da dake dake ko markade a bulanda me take yi mata. Ita kuma tana kula da girkinta da kuma hada lemummukan da ta san mijinta yafi so da sha'awar shi. Karfe biyu taje ta yi salan wayar Haidar ta sake shigowa bugowarsa ta hudu kenan bayan tashinta daga bacci. Ta dauko "Hello Honey, na baka gajiya da yo waya ko"? ❤❤❤SALON SO❤❤❤ ❤❤❤ PART 40 ❤❤❤ . BY SULAIMAN BOMBOY . Bebyna ya za ayi na gaji da jin muryarki hasken zuciyarta tare da jin lafiyarsu ita da bebyna. Ta yi shashshekar dariya cikin kissa da jan hankali ta makale murya tare da lankwasar da murya ta yi masa magana cikin yanga da marairaita. "Honey na ka kwantar da hankalinka kalau muke ni da bebynka, sai dai muna kewar dumin jikinka na dan lokaci." "Okey, beby na kada ki damu karfe hudu zan dawo gida mu kasance tare zuwa wayewar gari ko beby na?" Ta ce "Um hum thank you Honey na, sai ka dawo muna jiranka. Ya sumbaci wayar ya huro mata isa ta cikin wayar, ta shashshekar dariya da ta saukar wa da Haidar matsananciyar kasala yayi saurin ajiye wayar tare da jan diguwar ajiyar zuciya. Jawahir ta mike ta koma kicin ta debo fulas fulas dinta ta malmala tuwon farar shinkafarta da ya tuku ya yi luku luku da shi, kowanne ta malmala sai ta sa alaida sannan ta jera acikin fulas din. Ta juyo hadaddiyar miyar wake da ganye wadda ta dahu da hanta da koda da manja sai dan man kuli kadan lallai jawahir kin iya hada abin da zai kara muku jini da lafiya. Ta juye farfesun kifi irin ragon ruwan nan ta zai zuba kamshi yake yi, ta bude oben ta zaro gasashen naman ta da ya ji tumatir da albasa gashi yayi ruwa ruwa sai zuba kamshin kayan kamshi yake yi. Ta hada lemon kwakwa da madara sannan ta hada lemon abarba. Kowanne ta zuba a jug ta cilla kankara ta rufe ta kwashe kayan taje ta jere su a kasa yanda suke yi yanzu saboda girman cikinta. Iya ce ta gyara mata kicin din da duk wajen da ya baci. Jawahir ta shiga toilet ta tsalo wanka tare da tsala kwalliya ta shafe shafe da hadaddun kamshi na tururuka daban daban, simpil doguwar riga ta saka me rubi biyu sai walwalin dutsunan jiki ne suke ta zuba sheki. Ta dora sirrin mayafin akanta, ta futo falo ta zauna akan kafet ta mimmike kafafuwanta ta wara su yayin da ta jawo rumote ta latsa TV ta kama, ita kuma ta jingina da kujera tana kallo. Haidar ya turo kofar tare da sallamar tasa, ya yi saurin karasowa in da take ya zube a gabanta, ya tarairayo ta jikinsa "beby na" ya shafa mararta ya ku ke ya beby na yana dawo na same ku beby na komai lafiya ko?" Cikin murmushi take daga kai tana amsa masa tare da shafar sumarsa ta kansa. "Sannu beby na zauna anan kada ki tashi na hau sama na watso ruwa na zo mu fita muje mu ci abinci ko, ta daga kai. Ya mike ya yi sama da sauri ya fada toilet be jima ba ya fito ya shirya cikin kananan kayansa ya sakko, ta mike ta taro shi ya rungume ta a barin damansa "Muje restaurant mu ci abinci ko.?" Ta langabe a jikinsa "Haba my love da raina da lafiyata na kasa yi maka girki har sai ka fita waje ka ci? Honey na na yi mana girki." Ya rike baki "Bebyna bana hana ki wahalar da kanki ba? Daidai sanda suka zauna gaban kayan abincin yana bubbudawa, ta ce "Wallahi Honey na ba na son naga ka ci girkin waje ko na wani wajen, shi yasa nake daurewa na yi maka da kaina." "San kyau bebyna, na gode Allah ya yi miki albarka, ya raba ku da cikin nan lafiya" Amin Honey na gode." Suna cin abinci Haidar yana zuba santi, jawahir tana kyalkyala masa dariya. Da haka suka gama Haidar ne ya kwashe kayan, ya dawo ya same ta ta kwanta kan kafet ya durkusa kanta yana yi mata tausa sannu sannu yake matsa mata jikinta tare da mulmula mata bayanta a hankali ta ke fadin "wash, wash, tana limshe ido na son yin bacci. Karar wayarsa ce ta sa ta bude ido, ya dauka "Hello Inna kina lafiya kwana biyu?" Inna ta ce, "Lafiya lau nake ina jawahir din?" "Ga ta kusa da ni." "Yauwa daman dai kan maganar da nafara yi maka ne, zan zo na taho da jawahir don ta yi wankan gida". "Haidar ya katse ta da "Haba Inna saunawa zan gaya miki ne ni matata babu inda zata duk girman gidan nan bai ishe ta wanka ba sai kun dauke min ita, wanne hali kuke son saka ni?' Ta daka masa tsawa "Kai marar kunya bana son shashanci, haihuwar farin zaka yi wa wauta yaushe zamu barta ko mu ma wayaye ne irin ka.? Ta kife wayar tana mita. Jawahir ta dora kanta akan cinyar Haidar tana shafa fuskarsa. "Honey na me yake faruwa ne, don Allah ka daina damun kanka." "Bebyna ba dole na damu kaina ba, suna kokarin raba ni da ke, bebyna wai za ki iya tafiya wankan gida ki bar ni a nan har tsawon kwana arba'in da 'yan kai? Ta girgiza kai cikin yanayi na tausayi da son ta yi kuka "Honeyna ba zan barka ba bazan yarda su raba ni da kai ba, babu in da zan bi su." Daidai lokacin da ta dafe cikinta tana wash, wash!, yayi saurin rungumarta cikin rikita yana cewa, "Bebyna menene, me ya faru da cikin nawa.? My love bayana, cikina, kuguna, duk ciwo suke yi." Da sauri ya buga wa direbansa waya ya ce ya fito da mota zasu asibiti. Ya dakko jawahir direban ya bude musu bayan mota suka shiga, ya rife ya ja suka nufi asibitin, abinka da lafiyayyen asibiti tuni suka shigar da ita dakinta daban ita kadai a ciki Haidar ya furgice ganin yanda jawahir take wahala, gani yake kamar ciro cikin ya dawo da shi jikinsa shi ya yi nakudar ya haihu. "My love" ta kirawo shi maganarta kasa-kasa ya durkusa kanta yana jinta "My love kayi waya su Mama su zo kada na mutu basu ganni ba. Ya sake rungume ta yana ta mulmula mata bayanta, "Ki yi hakuri bebyna, ba za ki mutu ba kin kusan haihuwa. Idan ki ka haihu sai na yi musu waya su taho da kwarin gwiwarsu yanzu kuwa idan na gaya musu hankalinsu tashi zai yi su zo su cika asibitin ai ta damunki. "Wayyo Honey." Ta kankame shi tana nishi likitocin da suke kanta suna gaya mata ta yo nishi suna danna mata cikin a hankali tana yo nishi jariri ya fado tare da tsala kuka. Haidar ya yi saurin daukansa a cikin jinin ya na ta murna. Likitar ta yanke masa cibiya ta karbe shi ta mika wa nas don su gyarashi Wata sabuwar nakudar jawahir ta kama ba jumawa ta sunkuto 'ya mace ba da jimawa ba wani da namijin ya kuma futowa. Ikon Allah, Allah mai baiwa, Allah mai kyauta, har da kari jawahir ta haifi 'yan uku maza biyu mace daya, 'ya'yan kyawawa kamar 'ya'yan indiyawa don kyau da ja, Haidar duk ya rikice don murna waya yake ta bugawa kawai baya tsayawa gaisuwa sai dai ya basu labarin jawahir ta haifa masa kyawawan 'ya'ya har guda uku. Kafin ki ce meye wannan, tuni asibitin ya cika ya zama filin barka barka tare da murnar samun wannan kyawawan karuwar da aka yi. Kwanansu daya a asibiti aka sallame su don ba sa mun hutun suke ba saboda jama'a da suke ta tuttudowa ganin wannan kyauta da Allah ya yi musu da ba kowa ake ba wa ba. Nan kuma gaddama ta kaccame in da Inna ta daga gida za a yo da jawahir da jarirai shi kuma Haidar ya ce babu in da za 'a kai masa mata da 'ya 'ya, sai da Abbansa ya daka masa tsawa ya nuna masa bacin ransa a zahiri sannan ya bari aka tafi da su jawahir da yaran gidansu. Shi kuma Haidar ya yi fushi ya yi nasa gidan ransa a bace, yana shiga gidan yaga bakinsa yau ba jawahir a ciki can kuma ya rinka hango ta tare da 'ya 'yansa 'yan uku, haba wa, tuni wani sabon farin ciki ya sake mamaye shi ya shiga wanka ya sake sabon wanka ya zira farae shaddarsa sabuwa kal mai laushi sai sheki take yi kamar boyel. ❤❤❤SALON SO❤❤❤ ❤❤❤ PART 41 ❤❤❤ . By SULAIMAN BOMBOY . Ya debi makudan kudi wanda ba zan iya cewa ko na wane ba ya zuba a jaka ya fice ya kulle ko ina na gidan ya fito ya kara gaya wa megadi ya kula da gida sosai Ya shiga mota da kansa yake jan motar cikin farin ciki da annushuwa wani tsadaddaen hadadden kanti yaje wanda duk kayansu da ga waje suke shigowa da shi. Nan da bude bakin aljihu ya runka jidar kayan jarirai su tawul, da shawul da riguna famfas su safa da takalman jarirai komai iri daya guda uku yake kwasa, sai da ya cika but da kayan jarirai har da gadaje set me uku na jarirai. Haidar ko ya manta ne da dinbin siyayyar da suka yo daga kasar waje ta jariran ne? Oho. Ya je ya siyo katon ragonsa wanda za a yanka saboda naman gashi ya siyo kwandunan tattasai da tumatir da attaruhu albasa da kaji da zabi saboda girkin 'yan barka ya yiwa direbansa waya ya taho da wata motar kwashe wasu kayan suka nufi gidan su jawahir. Tirkashi! Wani aiki sai masu da shi, aka rinka jidar kayan da Haidar ya kawo ana kaiwa sashen momy Haidar ya shigo yana ta gaisawa da jama'a suna yi masa barka. Ya karasa falon Momi ya gaida su Momi su Anti Babarsa da su Inna da kannansa 'yan biyu. Dangi dai rankacakaf kowa ya zo, jariran suna hannunsu sun sha ado, da tsadaddun kaya 'yan kantuna masu kyau. Sayyada ce take gaya masa ai jawahir tana sashenta ta ce kada abar kowa ya shiga bacci zata yi, shi yasa aka kwaso jariran ma aka yo nan da su, saboda yan barka. Haidar ya ce ai suma jariran suna bukatar hutu da a kyale su aka yi a jikin uwarsu suna jin diminta suma suyi vaccin iya in an jima su ka tashi duk me son ganinsu sai ya gansu. Anty babarsa ta watso masa harara yayin da ya mike sum-sum ya bar falon ya nufi sashen da aka ware wa jawahir. Ya tura kofar falon ya shiga ko ina a gyare sai uban kamshi da yake tashi, yana kai cikin dakin wani kalar kamshin ya ja mai dadi da sanyaya zuciya. Ya hangota kan makeken gado tana ta baccinta hankalinta kwance. Ta yi kwanciyarta cikin jar sup me zanen ganye ta kara kyau da haske sai dai ta rame. Ya karasa bakin gadon ya sumbace ta yana shafa fuskarta tare da hura mata iska a kunnanta. Ta bude ido tare da fadada murmushinta "Lah, Honey ka daina fushin ka zo? Ta tashi ta jingina a jikinsa ya rungume ta yana shafarta tare da shakar ni'imtaccen kamshin da yake jikinta. Ya ce "Bebyna ai ba zan iya fushi da ku ba, ina zan iya bacci ba tare da naji diminki ba, ai ba ni da kwanciyar hankali in banga 'yan ukuna ba. Aka kwankwasa kofar jawahir ta yi saurin kwace kanta ta matsa can gefe, ta yi izinin a shigo. Inna ce da sajida suka shigo dauke da kwanukan abinci. Inna ta sakko mata da filo kasa ta ce zauna anan ta bude mata kwanon tuwon dawa yana turiri ta bude miyar kubewa danya da aka burge kaza ciki. Daya kwanon kuma gasasshen nama ne ya ji kayan kamshi da yajin daddawa. Sai kunun kanwa a kwanon sha Inna ta debo man shanu ta zuba mata amiyar ta ajiye mata yajin daddawa, ta ce "Sakko ki zauna maza ki cinye." Idon jawahir ya yi rau rau zata yi kuka, Haidar ya ce "Haba Inna daman dan ki yi mata izaya da badin tuwo da kunu shi yasa kika dage sai ta taho nan.? Inna ta ce, "Da Allah i min shiru ku me kuka sani wannan ai shine gatan me jego shi zai sa mata koshi ta sami wadataccen ruwan nono da 'ya 'yan zasu sha su koshi ko kasan har yanzu yaran basu sha komai ba sai zam zam da dabino? Cikin tashin hankali Haidar ya ce "Inna saboda me? Bayan an siyo musu katon din madara.? Inna ta ce, "Ai duk wani abu da za'a basu shi yanxu shirme ne in dai va su fara shan nonon uwarsu ba, nonon uwa shi ne abu mafi mahimmanci ga jariri. Don shi yake sa su kuzari yake kara musu lafiya kuma don haka ki sauri ki ci ga ruwan wanka can yakusa tafasa, idan an daki nonon da ganye zai temaka wajen zuwan ruwan nonon da sauri Haidar ya ce "A to ta so maza ki ci tuwon nan ki sha kunun. Jawahir ta kalli Haidar a marairaice alamun tsoro a faskarta. Haidar ya kamo hannunta "Yi hakuri ta so na taya ki ci kin ji kada ki damu. Ta zauna kan filon shi kuma ya zauna kan kafet din suka zuba yajin daddawa da man shanu suka fara cin tuwo. Yanda suka za ce shi ba haka suka ji ba, ashe dai shima tuwon dawar da dadi. Tun suna ci suna hira har abin ya kaisu da shiru sai dai gyada kai, kawai suke yi suna kai loma tare da zuba santi. Inna tana zaune tana kallon su sai da suka kusa cinye tuwon nan, Inna ta zazzuba musu kunan a kofina ta tura musu gasashen naman shima sun ci amma ba da yawa ba saboda koshin da suka yi. Cikin kwana biyu ruwan nonon jawahir ya watada tana shayar da 'ya 'yanta su koshi sosai. Daddare dai ba sa shan nono sai madara yau kwana hudu da haihuwar an kawo kayan barka akwati biyar na me jego da jirajirai. Bayanin kayan da suke ciki zai cika min dan lattafin nawa ban gama ba, hade da mukulun dankareriyar mota jif, me ruwan ganye wadda Haidar ya yiwa jawahir kyautarta da takardun dankareren gida da yake a Nasarawa GRA shima gift ne ya bata duk saboda haihuwar 'yan uku. Sai takardun filaye guda uku kowacce da sunan yaran mallakarsu ce kyautar ubansu Haidar da yake ba su. Kowa ya kalli kayan sai ya yi murna tare da son barka da wannan hidima da Haidar ya yi. Ranar suna an sa wa jariran mazan sunan baban Haidar da baban jawahir macen kuma an sa mata sunan Inna. Amma duk an boye musu sunan ana kiransu da Salim, Sadat, Salma, Alhamdulillahi taron suna ya yi kyau ya kuma kayatar ya burge kowa da yamma aka je dan Haidar da jawahir sun yi shigar kaya iri daya jawahir ansha gwala gwalai hannu da wuya da kunne har da sarkar kafa, sai sun jero a gurin fatin suna rike da hannun juna suna tafiya sannu sannu suna murmushi tare da hira kasa kasa a tsakaninsu sai sheki suke yi kamar taurari, Bayan su kuma Sayyada ce da Sajida sai Auwalu a tsakiyarsu suna dauke da jariran yaran an yi musu kwalliya ta ke ce raini Salma ta sha adon gwal har da siririyar sarka ta kafa da ta hannu masu bidiyo da hoto sai haskasu suke yi Sa'adu Bori ya saki kida yana wake su cikin wakar soyayya ta yi dadi Jawahir da Haidar. Allah ya raya Salim, Salma, Sadat, 'yan uwa kuwa suka balle bakin jaka sukai ta yi musu ruwan kudi. 'Yan uwa da abokan arziki suka rinka ba wa jawahir kyauta iri iri ta kayan jarirai da kudi da sauran su da haka taro ya watse. Kowa ya nufi gida, jawahir tana zaune a gidansu ita da jariranta da Inna sai kakar babarta wadda ita take yi mata wanka. Anty Maryam kuwa ta dage da sake hada wa jawahir sababbin sinadarai na matse 'ya mace da kara mata ni'ima mace ta koma kamar bata san namiji ba. Haidar kuwa kwana kawai yake yi a gidansa da safe da ya gama shirinsa gidan su jawahir zai taho ita zata hada masa break ya ci ya dauki yaransa ya yi musu wasa sannan ya tafi office. Haka in ya dawo ma nan zai zo jawahir ta shirya masa abinci ya ci ya yi kat yai ta rainon 'ya 'yansa ya na yi musu wasa sai shadayan dare sannan zai koma gidansa. **** **** ***** Bari mu waiwayi Kausar don muga wace rayuwa take y ne." Kausar tun ranar da ta bar gidan Haidar ta sauka a gidansu Abuja. Iyayenta sun tare ta da murna amma ganinta da shirmin akwatuna sai jikinsu ya yi sanyi suka shiga tambayarta da lafiya? Kausar ta gaya musu karya da gaskiya na ciwon Haidar sannan ta mika musu takardar sakin da ya yi mata. Ba su ji wani zafin sakin da ya yi mata ba don su a ganinsu gwanda hakan da 'yarsu ta takura, 'yan aikinta suka shiga gyara mata wajen zama. Kwanaki kalilan a tsakani mahaifanta suka tura kano gidan Haidar don kwaso kayan Kausar suka tarar da gida a kulle sai megida ne yake yi musu bayanin ai ba kasar, sai gidan su Haidar din suka je suka yi wa Anty bayanin zasu kwashi kaya. Anty ta yiwa Yaya Abba waya yazo ta bashi mukullayen ta ce ya je ya bude musu gidan ya tsaya su kwashi iya kayansu. Haka kuwa aka yi, ya je ya bude musu ya jira suka gama kwasar kayansu ko tsinke basu bari ba, bayan yin iddar Kausar ta bude shafin zawarci in da manema kuwa suka yo mata ca! Ganin ta fito daga gidan mekudi ga ta kuma 'yar mekudi. Kausar abinka da goggiyar tuni ta kuma wanke fata ta tsunduma cikin zawarci. Manema da yawa sun firfito mata sai dai rashin sa'ar da ta yi, duk cikinsu babu saurayi, daga me mata daya sai me mata biyu. Hakan ne yasa ta riki Bomboy dinta. in da ya fito ya kawo kudin aurenta ba dadewa ba aka sa ranar biki an sha shagali da casu kamar na budurwa. Ta tare a gidan ta dake nan K/Maiyaki. Bomboy dai ya dauki matar sa kauthar kamar wata sarauniyaba abin da be ajiye mata ba na jin dadin rayuwar dan Adam. Ba ruwanta da girkin gidan kullum sai dai ya dauke ta zuwa hotal su ci abin da ransu yake so, ruwa sai da na roba wato swan. Kowanne lokaci firji dinta cike yake da kalolin abincin gwangwani da kalolin lemummuka. Tuni Kausar ta kara gogewa jin dadi da hutu ya kara samun mazauni kome sai dai 'yan aikinta su yi mata bata katabus koda yaushe aikinta kwanciya ko ci. Ana cikin haka ne aiki ya kuma mayar da iyayen Kausar kasar America. A lokacin kuwa Kausar da Bomboy ba sa kasar don haka bata sani ba don iyayen nata sun ta lalubenta a wayarta ba su same ta ba, sai sallahu suka bar mata gun 'yan aikinta suka daga zuwa America. (((((( SALON SO )))))) : KARSHE! . BY SULAIMAN BOMBOY . KARSHE! . Ranar da Bomboy da Kausar suka dawo da ga tafiya, 'yan aikinta suka gabatar mata da sakon iyayenta. Kausar har kuka ta yi don bakin ciki gashi wayarta da lambobin iyayen nata suke ciki ta fadi a wannan tafiyar da ta yi, don haka ba wata hanya da zata ji su ba damar ta yi musu waya kenan, ko su yi mata? Ga shi bata san address din su a American ba, bare wata rana ta kai musu ziyara dole ta dauki dangana da hakuri ta na me fatan Allah sa su zo nan kusa don ta ji cikakken address dinsu ko ta bisu su tafi tare. Ba dadewa Kausar ta gama da laulayin ciki me wahalar gaske bata iya cin abinci sosai ga azabar ciwon ciki da ciwon kai. Hankalin Bomboy ya tashi da ganin rashin lafiyartata. Ya kwashe ta suka nufi asibiti akayi mata tes da gwaje gwaje daga karshe likitan ya dauki fitsarinta ya ce, gobe a dawo a karbi ruzol suka taho a hanya ya yi mata siyayya fal irin na marasa lafiya ya dawo da ita gida. Da gari ya waye Bomboy da kansa ya je ya karbo sakamakon gwajin da aka yi mata hankalin Bomboy yayi fari da ganin wannan sakamakon Murna a gun shi da Kausar kuwa kamar su hadiye juna don murnar samun ciki Kausar ta fara kawowa Bomboy tsarabe-tsarabe, ta ce wannan ta ce wannan haka Bomboy zai je ya kwaso mata. **** **** ****** ***** Sannu sannu rayuwa ta juya ta juyawa Bomboybaya domin kudin hannunsa tas sun kare 'yan aikinta wuya ta ishe su duk sun gudu sun barsu, sai ga Kausar ta je ta na rokon matan yayun Bomboy da su taimaka su rinka sammata abincinsu, su kuma suka ce muddin tana so ta rinka cin abincinsu sai dai ta fito ta rinka girkawa don babu bawanta da zai rinka dafawa yana bata tana ci. Dole Kausar ta fito tana girkawa da safe koko ne za'ayi shi tsilulu saboda babu wadatacciyar gasara, rafin kofi ake rabawa kokon ga ba kosai da rana a jika garin kwaki a yayyafa a kasan roba yaro ma baya koshi bare babba. Da daddare datsar dawa za a tuka bakikkirin da koriyar miyar kuka wadda daga daddawa sai barkono a ciki. Kausar ga fama da ciwo ga shi yanzu cikin nata ya kai wata shida ya yanzu cin abinci ne da ita saboda cikin yana sata masifaffiyar yunwa. Ga abincin da ake bata baya isarta, ga rashin dadi haka take hakura ta tattura, ga shi duk ta yi baki ta rame ta kanjame ke ba kya ce 'yar hutu Kausar din da ba ce. Duk ta bushe sai kashin wuya da tsinin ciki gashi bata iya yin tuwon ba duk ranar da ta yi sai yai danye ko ya yi gudaji. Ga matan yayye da 'yansu si yi mata masifa sun dungure mata kai suna yi mata ba la'i, dole ta jure ta hakura take zaune don bata da gurin zuwa in ma ta fita ga iyayenta har yau bata samu labarin su ba, to ina zata samu kudi xuwa American ma bare ta binciko in da suke. Don kayan dakinta kaf ta sai da su ta ci abinci duniya kenan me juyi juyi. **** ****** ****** Jawahir watanta biyar kenan da haihuwa ita da 'ya 'yanta sun kara kiba da haske sun yi kyau jajir da su kamar 'ya 'yan Turawa. Kowa ya kalle su sai ya yi sha'awar cewa da ma dai iyalinsa ne. Haidar arziki ya ci uban na da, ya tanfatsa musu wani tsantsareren gida na gani na fada wanda duk wanda yaje gidan kallo abinda yake fadan shi ne aljannar duniya. Gidan ya tsaru iya haduwa ya hadu, yanda Haidar ya hadewa jawahir falonta da dakunanta ko na sarauniyar indiya albarka Dakin 'yan uku kuwa ke kya ce kamfani ne tsadadde na kayan wasan yara saboda kayan alatu da suke ciki, Haidar ya kara girman da murjewa ya zama Alhaji me tsananin kyau da kwarjini. Jawahir ta zama big madam cikakkiyar mace ga kyau ga hutu ga kwarjini 'yan 'ya'yayansu guda uku abin sha'awa tubarkalla, bul bul da su jajir da su gashinsu akanannade kamar 'ya'yan turawa. Mijinta ya sakar mata naira sosai don duk wasu takaddun kamfanoninsa da gidajensa da filayensa da duk wasu kadarorinsa suna hannunta. Baya yi mata geji akan komai duk wani abu daya kamata ya yi na game da biyan ma',aikatansa albashi na kamfanoninsa zuwa na gidajensu, ya ce Abbansa ya kwanta ya huta shi yake komai na gidansu. Jawahir ta kasance me taimakon talakawa da kaskantattu wadanta basu da watada, don haka gidan nasu kullum yake cike da 'yan neman alfarma. 'Yan uku suna da shekara daidai ta yaye su sun yi girma sunyi wayo gudunsu suke yi ko ina ga surutu kamar Aku. Suma hadadden falonsu duk sun ci kwalliya kamar masu shirin zuwa fati, Haidar yana ta wasa da 'ya 'yansa ya ta da kai da cinyar jawahir Salim da Sadat shiga iri daya akayi musu ta jins da T shirt fara da aka yi rubutu da ruwan gwal a gaban rigar. Salma ma tana sanye da dan jins dinta da 'yar riga, kunnanta da wuyanta yana sanye da yari da sarka kirar daimond 'yar xire, kanta ya sha kananan kalba da kanan ribon a jiki yaran sun yi kyau kamar 'ya 'yan turawa. Gaba daya yaran suna kan Haidar suna ta tsalle tsallensu a jikinsa, wayar ku sa da jawahir ta yi kara ta daga ta kara a kunnenta, "Hello yauwa Anty jawahir wallahi wata bakuwa ce tazo ta kafe lallai tana son ganinki. Jawahir ta ce "Okey ba damuwa kawo ta muna falon sama Ta dire wayar, bakuwar da tun shigowarta ta saki baki tana ta kalle kalle a cikin gidan babu abin da ya fi kayatar da ita irin tsantsara tsantsaran falon da suka rinka wuce su, jikinta bai kara yin sanyi ba, sai da suka shiga wani tsantsareren falo wanda ya hadu da kayan kyale kyale sai wata hadaddiyar matattatakalar bene wadda aka yi ta kamar da ruwan gwal. Kasan matattakalar shimfide yake da kafet, suka hau suka yi sallama falon suka shiga. Jawahir ta dago kai tare da amsa sallamar ta zuba wa matar ido, tana tunanin ina ta santa. Matar ta zube a gabansu tana kuka Haidar kuwa yana ta wasa da 'ya 'yansa be ma dago kai ba bare yasan wacece. Jawahir ta ce a'a baiwar Allah me kuma yake faruwa daga zuwa sai kuka ba tare da kin yi wani bayani ba." Ta kwanto yan kwananniyar'yarta daga baya wadda shimi ce kawai a jikinta saboda rashin sutura matar kuma atamfa da take jikinta duk ta kode ta jeme ga hadin baki a jiki matar ta ce "Ban yi mamakin yanda baku gane ni ba ni ce Kausar. Jawahir ta yi zumbur ta mike tana rike da baki cikin mamaki ta ce "Kausar ke ce rayuwa ta maida ki haka me ya faru dake Kausar ina iyayenki da mijinki.?" Kausar ta goge hawayenta ta shiga basu labarin iyayenta da halin da take ci, ta juya tana kuka tana rokon Haidar gafara Haidar ya ce "Ni wallahi ba komai don rabuwa da ke alheri ya zamar min don da ina tare da ke da ban sami zaman lafiya da kwanciyyar hankali haka ba." Ya mike goye da Salma ya dauki Salim da Sadat a kafadarsa ya shige ciki. Kausar ta bisu da kallo tana me sha'awarsu shi da 'ya 'yansa da matarsa da ta yi hakuri da yanzu itama tana cikin wannan daular. Jawahir ta girgiza kai zuciyarta cike da tausayin halin da ta ga Kausar. Lallai duniya zancan banza ce kana takama kai wani ne lokaci daya sai Ubangiji ya mayar da kai ba komai ba. Jawahir ta ce Kausar "Ki yi hakuri lamarin duniya kenan don haka ba a son daukan duniya da zafi. Ta mike ta shiga daki ta debo sababbin riguna kala takwas da turamen atamfofi kala hudu da dinkakku kwance kala shida, da kudi naira dubu hamsin ta kawo mata ungo wa'yannan kije ki yi amfani da su zan kuma sa abinciko min koda lambar wayar iyayen naki ne kin ji ko." Kausar ta rissina ta rinka godiya tana kukan murna. Jawahir sai da ta sa aka hada mata kayan abinci fal bayan but din mota tasa direba ya kaita har gida. Kausar tana komawa ta sai rishonta ta sai kananzir galan guda ta kai dakinta take girkinta ita kadai ita da mijinta suna ci ta daina kula abincin gidan Nan fa matan gidan da 'ya'yan gidan suka tusa ta agaba da habaici da bakaken maganganu ita dai bata kula kowa sai ta rinka kulle wajenta ma ta daina sauraronsu. Sati biyu a tsakani jawahir ta ba wa direbanta waya sabuwa da kudi dubu goma a ciki da lambar wayar iyayen Kausar ta ce ya kai wa Kausar. Direba ya kama hanya ya kai wa Kausar ta rinka murna tana kwarara wa direba godiya ta ce ya mika mata godiya wajen jawahir din kafin tazo. Direba yana tafiya, Kausar ta kulle dakinta ta buga wayar bugu uku ana hudu aka dauka. Muryar babanta ta ji ta fashe da kuka, "Dady, Dady nice Kausar kun gudu kum barni cikin halin kunci da wahala. Tana kuka tana gaya masa halin da ta ke ciki da ita da mijinta tace yanzu mijinta bashi da komai suna cikin kuncin rayuwa hatta lokacin da ta haihu bai yi mata komai ba, da yunwar da ta sha da bautar girkin da take yiwa matan gidan da irin tsangwama da cin mutuncin da ake yi mata har kawo irin taimakon da jawahir take yi mata da binkicen da jawahir ta yi ta samo mata lambarsu ta kawo mata sabuwar waya da kati na dubu goma a ciki duk ta gama gaya masa. Hankalin babanta ya tashi ransa ya damu ya ce mata kiyi hakuri da man kwanan nan muke son mu zo mu duba ki ganin mun shekara daya da baro Nigeria. Amma kisa idonmu a cikin satin nan muna tafe." Hankalin babarta da 'yan uwarta ya yi masifar tashi da jin halin da Kausar ta ke ciki, ai basu iya hakuri ba kwanakin ba cikin kwana uku suka dira a Nigeria. Iyayenta da 'yan uwanta har kuka suka yi jin halin da Kausar ta shiga, nan fa aka shiga bata kashi tsakanin Bomboy da iyayen Kausar da kyar suka samu ya sake ta. Bayan ya sake ta ne, ya shiga daki yai ta kuka har da ihu shi ya shiga uku. Yanzu yaya za ayi ya kuma wani auren?" Da kyar su Amal Junior da Jauhar M. Nas suka rarrasheshi. Suka zo suka ta yiwa jawahir godiya tare da sa mata albarka. Suka roki kuma Haidar gafara a bisa abin da Kausar ta yi masa ya ce "Ba komai ai ya yafe mata. Nan fa kyakkyawar alaka da zumunci ya kullu tsakanin jawahir da Kausar da kuma iyayensu. Satinsu uku a Nigeria suka daga da Kausar da 'yarta da iyayenta zuwa America. Cikin lokaci kankani Kausar ta murmure ta murje ita da 'yarta ssuka shiga shafe shafen da ya bayyanar masu da kyansu. Bata dade da gama idda ba manema suka fito mata in da ta sake auren wani mai mata daya da 'ya'ya uku. Ya riki kausar da 'yarta cikin gaskiya da amana in da suke zaman lafiya da abokiyar zamanta. Haidar da jawahir linkafa ta ci gaba sun zamo abin kwatance da sha awa a Nigeria suna da 'ya'ya biyar kenan 'yan uku Salma, Sadat, Salim sai Nana khadija da Mohammad auta. Rayuwarsu me burgewa da ban sha awa kowa ya shiga gidan baya son fita don ganin irin rantsattsiyar SALON SO, ya yarda suke shimfidawa a gidan. ********************** ⬇ ************************** ********** Ai Hausa Novels **************** *************************⬆ ********************** DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog. Visit > https://www.aihausanovels.com.ng Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post. Email > aihausabooks@gmail.com ******* FOLLOW US ****** Facebook: Ai Hausa Novels Twitter: Ai Hausa Novels Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafin ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu. ********************** ⬇ ************************** *************** Ai Hausa Novels **************** ********************** ⬆ ************************** KASH DAMA ANCE LAIFIN DADI KAREWA. DUKKAN YABO DA GODIYA SUN TABBATA GA UBANGIJI DA YA BANI DAMAR KAMMALA KAWO WANNAN LITTAFI KAMAR YADDA MUKA FARA. TSIRA DA AMINCI SU KARA TABBATARWA GA SHUGABA ANNABIN RAHMA (S.A.W), ALAYEN SA DA SAHABBAN SA. DA FATAN MUN KARU DA DARUSSAN DA MUKA GANI A CIKIN WANGA LITTAFI, ALLAH YASA MUYI KOYI DA MASU KYAWAWAN HALAYEN DAKE CIKIN SA YA KUMA TSARE MU DAGA AIKATA MUNANAN AYYUKA MAKAMANTAN NA WASU DA MUKA JI A CIKI. TOHHH!!! INA FATAN NIMA XAKU TAYA NI ADDU'AN SAMUN WATA MATAR TUNDA MAFARKI NA TA SUBUCE MIN WATO KAUSAR. SAI MUN HADE A WANI SABON LITTAFIN INSHA ALLAH.. WASSALAM.